Connect with us

Ilimi

ASUU za ta ware rana ɗaya don yin zanga-zangar lumana

Published

on

Ƙungiyar malaman jami’o’i ta Najeriya ta ce za ta ayyana ranar da ba za ta shiga aji ba a jami’o’in ƙasar domin bayyana rashin jin daɗinsu game da zargin da take yi wa gwamnatin tarayya na riƙe musu albashin wasu watanni.

Babban jami’in ƙungiyar mai lura da shiyyar Kano Farfesa Abdulkadir Muhammad ya shaida wa BBC cewa ƙungiyar ASUU ta yanke shawarar ne domin bayyana ɓacin ranta kan matakin da gwamnatin tarayya ta ɗauka na ƙin biyan mambobin ƙungiyar albashinsu na wasu watanni bayan sun janye yajin aiki.

Ya ce ”kowane reshe zai zaɓi rana guda da zai gudanar da taro tare da zanga-zangar lumana, domin nuna ɓacin ransu da rashin jin daɗinsu kan yadda gwamnatin tarayya ke ƙoƙarin mayar da malaman jami’o’i ma’aikatan wucin gadi”.

Ya ƙara da cewa ”ASUU za ta gudanar da taro a kowane reshe na ƙungiyar, inda kuma duka mambobin ƙungiyar za su hallara, bayan gabatar da laccoci a wajen taron, mambobin ƙungiyar za su gudanar da zanga-zangar lumana a cikin kowacce jami’a, sannan kuma a ranar ba za su shiga aji domin koyawa dalibai karatu ba’.

A cikin watan Oktoba ne ASUU ta janye yajin aikin da ta kwashe wata takwas tana gudanarwa.

1 Comment

1 Comment

  1. Pingback: Kotu ta tsayar da ranar da za ta yanke hukuncin ƙarshe a ƙarar da Gwamnatin tarayya ta shigar da ASUU | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Ilimi

Da ilimi ake samun kowace irin nasara a rayuwa – Dauda Lawal 

Published

on

Da ilimi ake samun kowace irin nasara a rayuwa - Dauda Lawal 

Da ilimi ake samun kowace irin nasara a rayuwa – Dauda Lawal

Daga Idris UMAR, Zariya

Gwamna Dauda Lawal ya halarci taron yaye ɗalibai karo na uku da na huɗu na Jami’ar tarayya, wanda ya gudana a filin taro na Jami’ar da ke Gusau a cikin satin da ya gabata

Mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris ne ya bayyana haka a cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Litinin a Gusau cewa, Gwamna Lawal ya shelanta bayar da gurbin karatu ga duk wanda ya zo na ɗaya a Jami’ar.

Cikin jawabinsa a wurin taron, Gwamnan ya yaba wa shugabannin Jami’ar game da yadda suka iya ririta ɗan abin da suke da shi, duk da ɗimbin ƙalubalen da suke fuskanta.

Ya ce, “Ina matuƙar farin cikin kasancewa da ku yau a wannan bikin yaye ɗalibai karo na uku da na huɗu a wannan jajirtacciyar Jami’a, Jami’ar gwamnatin tarayya ta Gusau.

Ina taya jami’ar nan murnar samun wannan nasara, duk kuwa da matsalolin da suke fuskanta tun lokacin da aka kafa ta. Ina kuma yaba wa iyaye da ɗalibai bisa sadaukarwar da suka nuna har zuwa wannan matsayi.

Muna sa ran samun makoma mai kyau kuma mai albarka duk da tarin ƙalubalen da muke fuskanta a matsayinmu na jiha kuma al’umma.

Muna yin addu’a kuma muna aiki ba dare ba rana don samar da makoma mai kyau. Duk waɗannan matsaloli za su wuce da izinin Allah Maɗaukakin Sarki.”

Gwamnan ya yi ƙarin haske kan ƙoƙarin gwamnatinsa na gyara harkar ilimi a Jihar Zamfara bayan kafa dokar ta-ɓaci a bara.

“A matsayinmu na gwamnati, mun ƙuduri aniyar ilimantar da duk ’ya’yan Zamfara. Ilimi shi ne ginshiƙin da ke haskaka ruyuwar ɗan adam.

“Mun ware maƙudan kuɗaɗe ga ɓangaren ilimi a cikin kasafin kuɗinmu na 2024 kuma muna fatan za mu kai ga babban matsayi a 2025, 2026, da 2027. Muna fatan cimma kashi 25 zuwa 30 na haɓaka tsarin ilimi.

Tare da samar da ingantaccen tsari a fannin da sarrafa albarkatun da ya ƙunsa, muna da ƙwarin gwiwar cewa za mu farfaɗo da ababen more rayuwa, ɗaukar ƙwararrun malamai, horarwa da sake horar da waɗanda ake da su.

“Za kuma mu ƙara yawan masu karatu a makarantun firamare da na gaba da firamare ta hanyar wayar da kan jama’a da samar da ingantattun wuraren koyo da koyarwa. Ilimi kyauta ne, kuma muna fatan ya zama wajibi ga kowa.

“Mun kuma yi wa manyan makarantunmu da ke jihar kason kuɗi mai yawa don fara aikin gyara su zuwa matakai masu inganci.

KU KUMA KARANTA:Gwamnan Kaduna zai ba da ilimi kyauta ga ɗaliban Kuriga

A karon farko Jami’ar Jihar Zamfara na shirye-shiryen amincewa da shirin Hukumar Kula da Jami’o’i ta Ƙasa.

Mun umurci ’yan kwangilar da gwamnatin da ta shuɗe ta tilastawa barin wuraren aiki da su koma bakin aiki, kuma muna fatan nan da watanni masu zuwa, rukunin dindindin na jami’ar zai fara aiki. A lokaci guda, NUC za ta amince ga duk kwasa-kwasai.

“Mun karɓi mulki a jihar da gwamnati ta ƙi biyan kuɗaɗen jarrabawar WEAC da NECO har na biliyoyin Naira fiye da shekaru uku.

Dole muka yi shiri na musamman da hukumomin, kuma tun daga lokacin an fara biyan kuɗi a kan kari kuma za a kammala su a kan lokaci.

“A cikin ƙarancin albarkatunmu, za mu ci gaba da bayar da taimako ga jami’a. Burinmu shi ne mu ƙara haɓaka ilimi a jiharmu ta yadda za a samu damarmaki ga ɗaukacin matasanmu da za a horar da su don kai ga ƙololuwar da ilimi ke samarwa.”

Continue Reading

Ilimi

Jami’o’in Birtaniya za su fara ɗaukar masu sakamakon jarabawar NECO

Published

on

Jami’o’in Birtaniya za su fara ɗaukar masu sakamakon jarabawar NECO

Jami’o’in ƙasar Birtaniya na shirin fara daukar daliban Najeriya masu shaidar jarabawar kammala sakandare ta NECO.

Shugaban hukumar shirya jarabawa ta kasa (NECO), Farfesa Ibrahim Wushishi, ya ce Jami’ar Lead da Jami’ar Birmingham City da ke kasar Birtaniya sun tuntubi hukumar  kan jarabawar da take shiryawa.

Ya ce  jami’o’in sun fara tunanin bai wa daliban Najeriya gurbin karatu da sakamakon jarabawarsu ta NECO.

KU KUMA KARANTA: JAMB zata duba yiwuwar amfani da wayoyin hanu a jarabawar UTME

A fahimtarsa, hakan na nuni da  amincewa da ingancin sakamakon jarabawar NECO ne a idanun manyan jami’o’in ciki da wajen Najeriya.

Farfesa Wushishi ya bayyana hakan ne yayin wani taron tattaunawa da ’yan jarida a Abuja ranar Laraba.

Ya ce NECO ta cika sharudan Jami’ar Birmingham City, kuma a halin yanzu suna aiki tukuru kan ganin sun sami cika sharudan jami’ar Lead.

Continue Reading

Ilimi

Ƙungiyar ASUU ta yi barazanar shiga yajin aiki a jami’ar Maitama Sule

Published

on

Ƙungiyar Malaman Jami’o’i, ASUU, reshen Jami’ar Yusuf Maitama da ke Kano, ta koka kan rikicin da ke shirin kunno kai, idan har gwamnatin jihar ta gaza magance buƙatunta.

Ƙungiyar ta yi zargin cewa gwamnatin jihar ta shafe watanni tana yin watsi da buƙatunsu.

Hakan na ƙunshe ne cikin wata sanarwar haɗin gwiwa da shugaban reshen da kuma sakataren ƙungiyar Mansur Sa’ id da Yusuf Gwarzo suka sanya wa hannu a ranar Alhamis a Kano.

KU KUMA KARANTA:Zulum ya buƙaci Sojoji su samar da sansani a dajin Sambisa

Ya ce buƙatunsu guda uku ne waɗanda suka haɗa da inganta yanayin aiki ga mambobinsu.

Sauran kuma sun haɗa da bunƙasawa da kuma hanzarta samar da ci gaban jami’ar ta hanyar bayar da kuɗaɗen aiki mai ɗorewa, ƙarfafawa da kare ikon cin gashin kai na jami’a da ‘yancin ilimi.

Ƙungiyar ta ce ba ta so ta bayyana yanayin a fili ba amma ƙoƙarin da gwamnatin jihar ke yi na ganin ta biya musu buƙatunsu ya ci tura.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like