ASUU ta shiga ganawar sirri ta gaggawa

Shugabannin Ƙungiyar Malaman Jami’o’i ta Najeriya ASUU sun shiga ganawar sirri ta gaggawa.

Jaridar Daily Trust Najeriya ta ruwaito cewa ƙungiyar ta shiga ganawar sirrin ne da tsakar ranar Litinin, a harabar sakatariyar kungiyar da ke jami’ar Abuja.

Ganawar karkashin jagorancin shugaban kungiyar Farfesa Emmanuel Osodeke, za ta duba batun biyan malaman rabin albashin watan Oktoba.


Comments

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *