Connect with us

Labarai

Aƙalla mutum ’87’ aka sace a Kajuru na jihar Kaduna

Published

on

Wasu ƴan bindiga a Najeriya sun yi garkuwa da aƙalla mutum 87 da suka hada da mata da yara a jihar Kaduna, kamar yadda mazauna garin da ‘yan sanda suka bayyana a ranar Litinin.

Kakakin rundunar ƴan sandan Kaduna Mansur Hassan ya tabbatar da faruwar lamarin, wanda ya ce ya faru a ƙauyen Kajuru a daren Lahadi amma bai iya bayyana adadin waɗanda suka ɓata ba.

Wani hakimin ƙauyen, Tanko Wada Sarkin ya ce an sace mutum 87. “Ya zuwa yanzu mun sami labarin dawowar mutane biyar da suka koma gida da suka tsere ta cikin daji,” kamar yadda ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na Reuters ta wayar tarho.

Sace mutane da gungun masu aikata laifuka ke yi don neman a biya su kudin fansa ya zama ruwan dare kullum a Nijeriya, musamman a arewacin kasar, inda ake ganin hukumomi ba su da ikon hana su.

KU KUMA KARANTA: Ƴan bindigar da suka sace ɗalibai 286 sun buƙaci kuɗin fansa naira biliyan ɗaya

Wasu rahotannin sun ce ɓarayin sun kuma fasa shaguna da gidajen mutane suka yi sata.

Shi ma shugaban ƙaramar hukumar Kajuru Ibrahim Gajere ya shaida wa gidan talabijin na Channels cewa ƴan bindigan sun kutsa garin da misalin karfe tara na dare a ranar Lahadi.

Ya kuma koka kan yadda ake yawan satar mutane a Kajuru a baya-bayan nan, lamarin da ke sanya mutane cikin tsoro da fargaba sosai.

Ko a ranar 7 ga Maris, an sace daliban wata firamaren gwamnati 287 da hedimasta da wasu ma’aikata a karamar hukumar Kuriga a jihar Kaduna. Masu garkuwa da mutanen na neman kudin fansa domin su sako daliban a cewar hukumar makarantar.

Sai dai a ranar Asabar shugaban Najeriya Bola Tinubu ya yi gargadi game da biyan kudin fansa ga ‘yan fashi ko ‘yan ta’adda ko kuma masu dauke da makamai domin a sako mutanen da aka sace.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like