Connect with us

Al'ajabi

Yadda Fela ya auri mata 27 a rana guda a Legas

Published

on

A shekarar 1978, majagabam kiɗan Afrobeats, Fela Anikulapo Kuti, ya auri mata 27 a rana ɗaya, wannan ba abin mamaki bane ga waɗanda suka san rayuwa da salon na fitaccen mawaƙin Najeriyar da ake yi wa laƙabi da yaren Yarbanci da Abami Eda, wato halitta me ban mamaki.

An haifi Olufela Olusegun Oludotun Ransome-Kuti, a ranar 15 Oktoban 1938, ya rasu a 2 ga Agustan1997, sannan ana masa laƙabi da Abami Eda, mawaƙin Najeriya ne, makiɗi, ɗan gwagwarmayar siyasa, kuma ɗan kishin Afrika.

Ana ɗaukansa a matsayin majagaba na kiɗan da waƙe na Afrobeat, nau’in kiɗan Najeriya wanda ke haɗa kiɗan Afirka ta Yamma da funk na Amurka da jazz.

KU KUMA KARANTA: Tarihin Ali Jita da waƙoƙinsa

A lokacin da ya yi fice, an kira shi a matsayin ɗaya daga cikin “mawallafan kaɗe-kaɗe da kwarjini a Afirka”. All Music sun bayyana shi a matsayin muryar kiɗa da siyasa mai mahimmanci ta duniya.

Mahaifiyar Femi Kuti ta kasance ‘yar fafutukar kare haƙƙin matan Najeriya, Funmilayo Ransome-Kuti. Bayan samun ƙwarewa da horo a ƙasashen waje, shi da ƙungiyarsa ta Afirka 70 (wanda ta haɗa da daraktan kiɗa Tony Allen) sun yi rawar gani da nuna bajinta a Najeriya a cikin shekarun 1970s, a lokacin ya kasance mai sukar lamirin gwamnatin mulkin sojan Najeriya.

A cikin 1970, ya kafa ƙungiyarJamhuriyar Kalakuta, wacce ta ayyana kanta a matsayin bijirewa daga mulkin soja. Anyi fata -fata da yankin a cikin wani hari na 1978.

Da yawa daga cikin ‘yan ƙungiyar sun zama marayu, da kuma zawarawa marasa galiho, domin ya haɗa su tare, Fela ya yanke shawarar yin abin da ba a saba gani ba, inda ya bai wa mata ’yan ƙungiyar sa takarda domin rubuta sunayen waɗanda suke son aurensa; gaba ɗaya ‘yan ƙungiyar mata 27 suka rubuta sunayensu.

Bayan samun yardarsu, Fela Kuti ya auri matan su 27 a ranar 20 ga Fabrairun 1978, a otal ɗin Parisona da ke Anthony a Legas, tare da sanya albarkar limaman tsafi na Ifa su goma sha biyu.

Iyayen wasu daga cikin matan sun nuna damuwarsu da auren. Fela ya auri matan ne domin ya kula da su tare.

Ɗaurin auren ya samu halartar dangin Fela da abokansa da sauran ’yan ƙungiyar, kuma yayin daurin auren, Fela ya yi gajeriyar jawabi, inda yayi liƙin kuɗi a goshin matan nasa sannan ya ba su takardar shaidar auren.

Fela ya raba kwana a tsakanin matan nasa, wanda ya ƙunshi mata 12 a lokaci guda. Bayan daurin auren, Fela ya ɗauki matansa su 27 zuwa ƙasar Ghana domin hutun ma’aurata.

Gwamnatin Muhammadu Buhari ta kama Fela a shekarar 1984, ta ɗauresa, amma bayan wata 20 ta sake shi.

Sai dai a shekarar 1986, jim kaɗan bayan fitowarsa daga gidan yari, Fela Kuti ya saki matansa guda 27 bisa dalilin cewa aure yana kawo kishi.

Wani abin lura da birgewa shine babu wadda Fela ya tilasta wa barin gidansa bayan sakin, wasu sun zauna tare da shi har ya rasu a shekarar 1997.

Tun mutuwarsa a cikin 1997, ɗansa, Femi Kuti ne ke kula da sake fitowa da kuma harhaɗa wakokinsa.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Al'ajabi

An ƙona mutane suna Sallar Asuba a masallaci a Kano

Published

on

An ƙona mutane suna Sallar Asuba a masallaci a Kano

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano a arewacin Najeriya ta ce ta kama wani mutum da ake zargi da cinna wa wani masallaci wuta yayin da mutane ke Sallar Asuba ranar Laraba.

Lamarin ya faru ne a ƙauyen Gadan da ke Ƙaramar Hukumar Gezawa a jihar ta Kano, da misalin karfe 5:20 lokacin da ake sallah, a cewar sanarwa ‘yan sanda.

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Kano, Abdullahi Haruna Kiyawa ya tabbatar wa da TRT Afrika Hausa faruwar lamarin da kama mutumin da ake zargi, sai dai ya ce ana ci gaba da gudanar da bincike.

Abdullahi Kiyawa ya ce bincike ya nuna cewa mutumin da ake zargi da cinna wutar Shafi’u Abubakar mai kimanin shekaru 38 ya jefa wata roba ne ɗauke da fetur cikin masallacin, sannan ya cinna wuta.

KU KUMA KARANTA: Mahara a Anambara sun ƙona fadar babban Basarake ƙurmus

Kakakin ‘yan sandan ya ce mutum 24 ne suka ƙone a masallacin, da suka haɗar da manya 20, yara huɗu.

An garzaya da duka waɗanda suka jikkata zuwa asibiti don ba su kulawa, amma babu wanda ya mutu a haɗarin, a cewar sanarwar ‘yan sandan.

Continue Reading

Al'ajabi

An tsinci gawar wata ɗaliba a cikin ɗaki a Kano

Published

on

An tsinci gawar wata ɗaliba mai suna Aisha Yahaya ta Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Aliko Ɗangote da ke Wudil, a wani gida da ke wajen jami’ar.

Aisha, ɗaliba ce da ke matakin karatu na uku wato ‘level 300’ a sashen nazarin Kimiyya da Fasahar Abinci na jami’ar wadda aka tsinci gawarta bayan ta koma ɗakinta.

An ce ɗalibar ta rubuta jarrabawarta ta farko a zangon karatun na farko da ake yi a jami’ar.

Wasu daga cikin abokan karatunta sun danganta mutuwarta da shiga cikin matsi da damuwa a dalilin karatu da kuma zana jarrabawar.

A cikin wasiƙar ta’aziyyar, hukumar jami’ar ta bayyana matuƙar baƙin cikinta dangane da rasuwar Aisha Yahaya.

KU KUMA KARANTA: An tsinci gawar wani mutum a kan titi a Kano

Sanarwar ta ce, “Aisha ɗaliba ce mai hazaƙa wadda ta rasu a dalilin bugun zuciya. Za a riƙa tunawa da ita a kan sha’awarta na karatu da jajircewarta kan harkokin karatunta.”

Jami’ar ta ƙara da cewa, ba a iya gano wata da ke tattare da ita ba gabanin mutuwarta saboda ba ta nuna alamun rashin lafiya ko fama da wata cuta ba.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like