Connect with us

'Yansanda

Yan sanda za su sake fasalin tsaro a babbar hanyar Legas zuwa Ibadan

Published

on

Sakamakon karin bayanai kan yanayin tsaro dangane da babbar hanyar Legas zuwa Ibadan da kwamishinonin ‘yan sanda masu kula da jihohin Legas, Ogun, da Oyo suka isar wa babban sufeton ‘yan sandan Najeriya (IGP), Usman Alkali Baba, sufeton janar ya bayar da umarnin a sake yin gyare gyare cikin gaggawa domin sauya fasalin tsaro a kan babbar hanyar tare da sanya isassun jami’ai tare da kayan aikinsu don tabbatar da kare rayuka da dukiyoyi al’umma dake kai komo a kan hanyar tare da dakile sace-sacen mutane da sauran munanan abubuwan da ke faruwa a hanyar.

Hakan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa mai ɗauke da sa hannun jami’in hulda da jama’a na rundunar’yan sandan Najeriya CSP Olumuyiwa Adejobi wanda ya aike wa kafar yaɗa labarai ta Neptune Prime.

Hakazalika, IGP Usman Alkali Baban ya jaddada cewa hukumar ‘yan sanda ta damu da ƙalubalen tsaro da ake fama da shi a kan babbar hanyar, sai dai ta himmatu wajen tsara hanyoyin da za a bi don daƙile matsalar tsaro da kuma kawar da baraza a kan hanyar, ta yadda za a iya magance matsalar.

Don haka Sufeto-Janar na ‘yan sandan ya yi alƙawarin bayar da cikakken goyon bayan gudanar da aiki ta hanyar fasahar zamani da ƙere-ƙere tare da samar da kayan aiki ga kwamishinonin ‘yan sandan da ke kula da jihohin Legas, Ogun, da Oyo, da kuma shugabannin rundunonin gudanar da dabarun yaƙi a yankin domin yaƙar halin da ake ciki na laifuka da ɓata gari ke aikatawa a kan babbar hanyar ta Legas zuwa Ibadan.

Hakazalika, Sufeto Janar na ‘yan sandan ya yi kira ga ‘yan Nijeriya masu kishin ƙasa, musamman masu amfani da hanyoyin da mafarauta da shugabannin al’umma, da sauran masu ruwa da tsaki da ke bin wannan hanya da su riƙa tona asirin ɓarayin da ke addabar ‘yan Nijeriya da ba su ji ba ba su gani ba a kan hanyar, inda yayi kiran ga kuma maƙwabtan hanyar da al’umma da ke zaune a yankin da su dinga bai wa ‘yan sanda da sauran hukumomin tsaro bayanai domin kama ɓatagarin tare da gurfanar da su cikin gaggawa.

1 Comment

1 Comment

  1. Pingback: Almubazzaraci ya sa an kori ’yan sandan Imo bakwai, an gurfanar da su gaban kuliya | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

'Yansanda

‘Yan sanda sun kama matashin da ake zargi da yin garkuwa da ‘yar maƙocinsa

Published

on

'Yan sanda sun kama matashin da ake zargi da yin garkuwa da 'yar maƙocinsa

‘Yan sanda sun kama matashin da ake zargi da yin garkuwa da ‘yar maƙocinsa

Daga Shafaatu Dauda,Kano

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano, ta kama wani matashi mai suna Zakariyya Muhammad, da ake zargi da laifin yin garkuwa da ƙaramar yarinya mai shekaru biyu da rabi.

Kakakin Rundunar ‘yan sandan jihar Kano, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ne ya bayyana hakan ta cikin wata sanarwa da ya aike wa da manema labarai a ranar Talata.

Sanarwar ta ce, tun a Ranar 4 ga watan Yuli 2024, rundunar ta samu ƙorafi daga wani Mazaunin unguwar Sabuwar Gandu Kwarin Barka, cewar wani ya ƙira wayar sa inda ya shaida masa cewar ya yi garkuwa da ‘yarsa mai suna Amina , har aka nemi a biya shi kuɗin fansa naira miliyan biyu kafin ya sake ta.

Bayan samun korafin ne Kwamishinan ‘yan sandan jihar Kano, CP Salman Dogo Garba, ya tayar da dakarun ‘yan sanda ma su yaƙi da garkuwa da mutane, ƙarƙashin jagorancin SP Aliyu Muhammad Auwal, tare da ba Su umarnin kuɓutar da yarinyar cikin a wanni 24, da kuma kama waɗanda ake zargin.

SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya ƙara da cewa, an yi nasarar kama wanda ake zargin Zakariya Muhammad , a ranar 5 ga watan Yuni 2024, inda ya tabbatar da cewar shi ne ya yi garkuwa da yarinyar sannan ya nemi kuɗin fansa.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan sanda a Kano sun ceto ’yar shekara 2 da maƙocinsu ya sace

Neptune Prime Hausa ta kawo rahotan na cewa tuni aka kuɓutar da yarinyar kuma likitoci sun tabbatar da cewar kalau ta ke.

Kakakin Rundunar ‘yan sandan Kano, ya ce an dawo da batun babban sashin binciken manyan laifuka dake Bomapai, ɓangaren da ya shafi garkuwa da mutane, kuma da zarar an kammala bincike za a gurfanar da shi a gaban kotu.

Rundunar ta ja hankalin iyaye su dinga kula da ‘ya’yansu, tare da jan kunnen matasa cewar wannan ba abin yi ba ne, kuma ba sana’a ba ce, musamman a jihar Kano domun ma su yunƙurin aikata ba su da wajen ɓuya.

Continue Reading

'Yansanda

An ja hankalin ‘yan Najeriya kan shirin ƙungiyoyin asiri na ɗaukar sabbin mambobi

Published

on

An ja hankalin 'yan Najeriya kan shirin ƙungiyoyin asiri na ɗaukar sabbin mambobi

An ja hankalin ‘yan Najeriya kan shirin ƙungiyoyin asiri na ɗaukar sabbin mambobi

Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta ja hankalin ‘yan ƙasar game da shirin ƙungiyoyin asiri na ɗaukar sabbin mambobi a faɗin ƙasar musamman a jami’o’i da manyan makarantu.

Mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan Najeriya reshen Jihar Ribas Grace Iringe-Koko ce ta yi wannan jan hankali a cikin wata sanarwa da ta fitar ranar Asabar da maraice a birnin Fatakwal.

Ta bayyana cewa wata babbar ƙungiyar asiri ta Najeriya tana shirin gudanar da gagarumin biki ranar Lahadi a faɗin Najeriya, musamman a jami’o’i don tunawa da mutumin da ya kafa ta.

“Rundunar ‘yan sandan Jihar Ribas ta samu bayanai game da bikin da ƙungiyar Neo-Black Movement (NBM) za ta yi a faɗin ƙasar ranar 7 ga watan Yulin 2024. Ƙungiyar, wadda ake yi wa laƙabi da Aiye ko Black Axe, tana shirin gudanar da bikin ne domin tunawa da wanda ya kafa ta.

KU KUMA KARANTA: Shugaban hukumar leƙen asirin sojin Isra’ila ya yi murabus saboda harin Hamas na 7 ga Oktoba      

Bikin, wanda aka sanya wa suna Ranar AIYE ko 7/7 za a gudanar da shi ne a dukkan jihohin da ke faɗin ƙasa, musamman a manyan makarantu,” in ji sanarwar.

An gargaɗi masu ta da hankalin jama’a a Bikin Dodanni na Egungun a Jihar Oyo

Rundunar ‘yan sandan ta ce tana sane da munanan ayyukan ƙungiyar asirin na kisan mutane a manyan makarantu da faɗace-faɗace a tsakanin ƙungiyoyin asiri da tayar da zaune-tsaye da sauran manyan laifuka.

Ta ce yanzu haka ta baza ƙarin jami’an ‘yan sanda zuwa wasu wurare domin daƙile ayyukan ƙungiyoyin asiri, sannan ta yi ƙira ga iyaye su gargaɗi ‘ya’yansu su guji shiga ayyukan ƙungiyoyin asiri.

“Ana bai wa manyan makarantu shawarar ƙara matakan tsaro da kuma sanya idanu sosai domin tabbatar da tsaron dukkan ɗalibai.

Kazalika ana ƙira ga dukkan makarantu su lura da duk wani taro na ɗalibai da bai kwanta musu a rai ba,” a cewar sanarwar.

Continue Reading

'Yansanda

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

Published

on

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

Rundunar ’yan sandan Najeriya ta tube wa wasu jami’an ta biyar kaki sakamakon zargin su da karɓar cin hancin kuɗi kimanin Naira miliyan uku.

Mataimakin Shugaban ’yan Sanda mai kula da Shiyya ta shida ta da ke Jihar Kuros Riba, Jonathan Towuru, ya sanar a Kalaba cewa ’yan sandan sun kwace kuɗin ne da bakin bindiga a hannun wani mai abin hawa.

A makon jiya ne aka zargi jami’an da ƙwayar kuɗin da bakin bindiga a hannun wani mutum da rundunar ta sakaya sunansa.

Yanzu haka waɗanda ake zargin an tuɓe masu kaki amma ana tsare da su ana bincike, da zarar an same su da laifi kotu za a turasu ta yanke masu hukuncin da ya dace.

KU KUMA KARANTA: ’Yan sanda za su tantance ’yan banga a Yobe

Mataimakin shugaban ’yan sandan ya ce waɗanda ake zargin su da karɓar cin hancin kuɗi Naira milyan uku daga wannun wani.

Ko a kwanan baya irin haka ta taba faruwa a kan babbar hanyar Kalaba zuwa Ikom inda aka kama wasu ’yan sanda kan karbar na goro.

Tafiya a kan hanyar na yawan zargin ’yan sanda da kula da shingen bincike a kan hanyar da yawan tatsar su kuɗi.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like