Ruwan sama na kwana uku ya hana Kanawa fita neman na abinci

0
281

Daga Fatima GIMBA, Abuja

Al’ummar jihar Kano a arewacin Najeriya na ci gaba da bayyano ra’ayoyinsu dangane da yadda aka yi ta mamakon ruwan sama na kwanaki uku a jere.


Ruwan saman ya tsayar da harkokin ciniki da dama a babban birnin jihar. Ba kasafai ba dai ake samun mamakon ruwan sama da za a jera irin wadnan kwanaki har uku ana ruwa ba, da ya wuce awanni ba.


Wannan mamakon ruwan saman da aka samu a jihar ya jefa wasu daga cikin iyali halin ƙunci sakamakon rashin samun damar fita a samo abin kai wa baka saboda ruwan da ake yi.

Leave a Reply