Connect with us

Doka

Zan gurfanar da hukumar Hisbah idan bata ɗauki mataki akan mawaƙi Gwanja ba- Barista Gandu

Published

on

Daga Shafa’atu DAUDA, Kano

Wani lauya ɗan gwagwamarya mai zaman kansa a jahar Kano, Barista Badamasi Sulaiman Gandu ya rubuta takaddar ƙorafi akan wata sabuwar Waƙar Ado Isah Gwanja mai taken ‘’CASS ko Asosa’’ ga hukuumar Hisbah ta jahar Kano, dan ta ɗauki matakin gaggawa ga me da sabuwar Waƙar.

Barista Badamasi Gandu a cikin takaddar koken tasa, ya ce ‘’hakika Kano babban garin tarihi ne akan addini da tarbiya irinta addinin musulinci, har ya bada misalin cewa a makonnin da suka gabata wani matashi yaje kan Kabari ya yi rashin mutunci kuma nan ta ke rundunar yan sandan jahar Kano suka kama shi don ya girbi abinda ya shuka, wanda Baristan ya jinjina wa jami’an yan sandan bisa wannan namijin ƙokari’’.

‘’Gandu ya kara da cewa sai gashi mun wayi gari da sabuwar waƙa ta fitsara da rashin kunya wadda tana ta yawo a gari, abun mamaki kowa ya yi shiru duk da ba kowa ne ya sami jin labarin Waƙar ba’.

‘’ya ce a matsayi na na ɗan jihar Kano mai kishin addinin musulinci bazan yi shiru ba.’’ inji Gandu, dan haka ne na ke kira ga hukumar Hisbah da ta ɗauki matakin gaggawa akan daƙile wannan musiba cikin gaggawa nan da kwana uku (3).’’

‘’Ƙin ɗaukar wannan mataki a cikin kwana uku (3) zan dau matakin gurfanar da hisbah agaban kotu mai cikkaken iko .’’

KU KUMA KARANTA: Muna Neman Safara da Mr 442 Ruwa a jallo- Afakallahu

‘’Barista Badamasi Gandu ya yi kira ga mai girma gwamnan jahar Kano, kasancewar sa khadimul Islam mai kuma kishin addinin musulinci, akan Gwamnatin jahar Kano ta ɗauki Ado Isah Gwanja kasancewar haziƙin mawaki aiki a hukumar Hisbah ta jahar Kano, a bashi horo ta yadda zai juyar da basirarsa wajen aikin DA’AWA. Kasance war Gwamnan musulmin ƙwarai, kuma mai daraja da kishin addini, zai aminta ya kuma bawa addini gudunmawa, tare da kiran malamai su tallafi wannan kiran nasa.’

A ƙarshe Badamasi ya nuna takaicinsa na yadda hotunan fitsara da rashin mutunci suke yawo a shafukan sada zumunta a faɗin ƙasar nan wadanda sun saɓa da al’adar mutane da kuma addinin su.

Lawyan yayi kira ga ministan sadarwa, Farfesa Sheik Ali Isah Ibrahim Pantami da ya ɗauki matakin daƙile irin waɗannan waƙoƙi da hotuna, tare da kawo tsarin da hotunan za su daina hawa matukar sun saɓa da al’ada da kuma tarbiyar al’umma.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Doka

Kotu ta umarci jihar Ondo da ta biya diyyar naira miliyan 30 ga mutumin da ‘yan Amotekun suka harbe

Published

on

Ta kama mijinta yana lalata da ’ya’yan cikinsu

Wata babbar kotun Ondo da ke zamanta a Akure, a ranar Larabar da ta gabata ta umarci gwamnatin jihar Ondo da ta biya wani Oluwasegun Oluwarotimi kuɗi naira miliyan 30 a matsayin diyyar harbin bindiga da ya samu a wata arangama da jami’an tsaro na jihar, wanda aka fi sani da ‘yan Amotekun.

Oluwarotimi mai shekaru 36, mai tuƙa babur ne, wato ɗan okada ne lokacin da lamarin ya faru.

A nasa jawabin, Mai shari’a Adejumo ya bayar da umarnin a biya Oluwarotimi kuɗi naira miliyan talatin a matsayin diyya.

KU KUMA KARANTA: Hukumar NYSC ta biya diyya ga dangin ɗan bautar ƙasa da ya ɓata

Oluwarotimi, wanda a yanzu an yanke shi ne sakamakon harbin da aka yi masa ba bisa ka’ida ba,inda ya shigar da karar a gaban kotu.

“B bisa ka’ida ba a titin Araromi a ranar 9 ga watan Agustan 2021 a Akure, harbin da Amotekun ta yi ya saɓa wa hakkin ɗan Adam.

“Kotu ta umurci waɗanda ake ƙara da su hada kai su biya Naira miliyan 20 ga wanda ake kara a matsayin diyya na gaba daya da kuma Naira miliyan 10 a matsayin diyya ta misali,” in ji alkalin.

Continue Reading

Doka

An sanya dokar hana fita a Kano

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta sanya dokar ta-ɓaci har zuwa faɗuwar rana don kaucewa taɓarɓarewar doka da oda, biyo bayan tattara sakamakon zaɓen gwamna da na ‘yan majalisar dokokin jihar.

Kwamishinan yaɗa labarai da harkokin cikin gida na jihar, Malam Muhammad Garba ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar da safiyar Litinin.

KU KUMA KARANTA: Yadda Abba Kabir Yusuf na NNPP ya lashe zaɓen Kano

Ya ce an yanke shawarar ne don hana ’yan daba su haifar da hargitsi a halin da ake ciki.

Kwamishinan ya yi kira ga jama’ar jihar da su kasance a cikin gida domin jami’an tsaro ba za su ƙyale kowa ko wata ƙungiyar da ke da niyyar haddasa fitina ba.

Continue Reading

Doka

Kotu ta sanya sharudɗa akan batun bada belin doguwa

Published

on

sharudɗan sune kamar haka:

Kotu ta haramtawa Alhassan Ado Doguwa zuwa mazaɓarsa ranar zaɓen ta gwamna da ‘yan majalisar jiha.

Wannan dai na cikin sharudɗa da babbar kotun tarayya ta sanya kafin bada belin Alhassan Ado Doguwa.

Ga dai ƙarin jerin sharudɗan da kotu ta sanya kafin bada belin.

1- Zai ajiye zunzurutun kuɗi har naira miliyan 500

2- Gabatar da sarki mai daraja ta ɗaya a matsayin wanda zai tsaya mishi.

KU KUMA KARANTA: INEC ta cire sunan shugaban masu rinjaye, Doguwa daga jerin sunayen ‘yan majalisar wakilai

3- Gabatar da babban sakatare a gwamnatin jiha ko ta tarayya a matsayin wanda zai tsaya mishi.

4- Zai ajiye Fasfo da sauran dukkanin takaddunshi na tafiya a kotu.

A karshe kuma kotu tace bazai halacci mazaɓarsa ba yayin zaɓen gwamna da yan majalisun jiha dake tafe.

Ko ya kuke kallon wannan batu?

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like