Connect with us

Zaɓe

Za mu shiga zaɓen ƙananan hukumomi a Yobe — Jam’iyyun Adawa

Published

on

Mun shirya tsaf domin shiga wannan zaɓe amma kuma muna sara ne muna duba bakin gatarinmu.

A yayin da ake ci gaba da shirye-shiryen gudanar da zaɓen ƙananan hukumomin a ranar Asabar ta ƙarshen wannan wata na Mayu a Jihar Yobe, wasu shugabannin jam’iyyun adawa da ke jihar da suka haɗa da Jam’iyyar NNPP da PDP da AD da PDM sun bayyana shirinsu na shiga wannan zaɓe matuƙar za a ba su damar shiga takarar ba tare da an yi musu ƙwange ba.

Shugaban Jam’iyyar NNPP a Jihar Yobe, Alhaji Yakubu Shehu Damagum ya bayyana cewa, jam’iyyarsu ta NNPP a Jihar Yobe ta shirya tsaf don shiga zaɓen ƙananan hukumomin matuƙar Hukumar Zaɓe ta Jihar Yobe ta amince ta sayar musu da fom ɗin tsayawa takara.

Shugaban ya ce, Jam’iyyar NNPP ba ta wata tantama a kan shiga zaɓen, kamar yadda wasu ke cewa jam’iyyun adawa a jihar ba za su shiga zaɓen ba, inda ya fito ƙarara ya ƙaryata wannan magana.

Ya ƙara da cewar, babban abin da ke gabansu shi ne samun fom ɗin tsayawa takarar daga Hukumar Zaɓen jihar da kuma samun ainihin ’yan takarar da ke da sha’awar tsayawa takarar.

Ya bayyana cewa domin kuwa ya zuwa yanzun ɗan takara ɗaya tak suka samu na kansila daga Ƙaramar Hukumar Karasuwa, wanda shi kaɗai ne ya zuwa yanzu ya fito ya nuna sha’awarsa ta tsayawa takara a duk Jihar Yobe, amma ba su san nan gaba.

Shugaban na NNPP ya ƙara da cewar, tuni Jam’iyyarsu ta NNPP ta tura takardarsu zuwa Hukumar zaɓe ta Jihar Yobe domin bayyana shirinsu na shiga zaɓen.

Shi ma Shugaban Jam’iyyar AD, Malam Habu Doro Potiskum bayyana wa Aminiya matsayarsu a kan cewa, su ma a shirye suke su shiga cikin wannan zaɓe na ƙananan hukumomi a Jihar ta Yobe, amma kuma suna sara ne suna duba bakin gatarinsu, domin ba zai yiwu a ba su ga ana aikata ba daidai ba kuma su zuba ido, kasancewar akwai amanar al’umma a kansu.

KU KUMA KARANTA:Gwamnatin Yobe za ta mayar da kwale-kwalen Dufuna mai shekaru 8,000 zuwa cibiyar yawon buɗe ido

Ya ce, suna sane da cewar kai da kaya duk mallakar wuya ne, ma’ana da Hukumar Zaɓen jihar da ma’aikatanta duk mallakin Gwamnatin Jihar Yobe ne, inda ba za su taɓa yarda ’yan takararsu a kowane mataki su faɗi zaɓe ba, wanda hakan ke nuna cewar, in jam’iyyun adawa suka shiga ma, sun san yadda sakamakon zaɓen zai kasance.

Game da ko jam’iyyarsu tana da ’yan takara, sai shugaban ya bayyana cewa, zuwa yanzu ba su da ɗan takara ko da guda, wanda a ganinsa hakan ba ya rasa nasaba da tunanin da jama’a ke yi cewar, idan mutum ya fito ma bata lokacinsa da kudinsa kawai zai yi.

Ya ce kasancewarsu ’yan jam’iyyar adawa suna ganin cewa duk wanda ya fito takara ba lallai ba ne ya ci zaɓen, komai kuwa yawan jama’arsa, domin kuwa Hukumar Zaɓe ta jihar ita za ta shirya zaɓen kamar yadda kowace jiha ke yi.

A tattaunawarsa da menema labarai kuwa da Shugaban Jam’iyyar PDM a Jihar ta Yobe dangane da yiwuwar shigar jam’iyyar zaɓen ya ce, zuwa yanzu dai kam ba su yanke shawarar komai ba a kan yiwuwar shiga zaben ko kuma akasin hakan, amma za su sanar da matsayarsu nan gaba kaɗan.

A nasa ɓangaren, Shugaban Jam’iyyar PDP a Jihar Yobe, Sanata Umar El-Gash ya ce, shakka babu jam’iyyarsu za ta shiga zaɓen kuma za a fafata da ita, fata dai kawai shi ne a yi adalci.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

INEC

INEC ta dakatar da wani jami’inta don gudanar da bincike kan ɓacewar takardun kaɗa ƙuri’a

Published

on

Daga Maryam Umar Abdullahi

Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta Najeriya ta dakatar da wani jami’inta mai suna Mr Fred Ogboji, wanda ke kula da ƙaramar hukumar Jos ta Arewa, bisa zargin ɓacewar wasu muhimman kayayyakin gudanar da zabe.

Hukumar INEC, a wata sanarwa ta ce ta dakatar da jami’in nata ne don samun sukunin gudanar da bincike a kan ɓacewar takardun kaɗa ƙuri’a na kujerar majalisar wakilai na shiyyar Bassa da Jos ta Arewa a rumfuna goma sha shida, a ƙaramar hukumar Jos ta Arewa.

Jami’a a sashen yaɗa labarai na hukumar INEC, Zainab Aminu, ta tabbatar da dakatar da jami’in, don yin bincike.

Duk da umurnin sake yin zaɓen a ranar Lahadi a wasu rumfuna, jami’an zaɓe ba su fito a kan lokaci ba, yayin da a wasu rumfunan jama’a ba su fito don sake gudanar da zaɓen ba.

KU KUMA KARANTA:Ministan Wajen Turkiyya ya yi gargaɗi  kan yiwuwar ɓarkewar rikici, saboda harin da Amurka ke kai wa ƙungiyoyin da Iran ke goyon baya

Mr. Raphael Madugu, wani ɗan jarida a jihar Filato, ya ce sun yi ta ƙoƙarin samun jami’in hukumar zaɓen don ya yi bayani kan matsalolin da aka fuskanta a rumfunan zaɓen amma bai amsa ƙira da saƙonni da aka aike masa ba.

An gudanar da zaɓen Sanata na shiyyar Arewacin jihar Filato da na majalisar wakilai na Jos ta Arewa da Bassa ne bayan da kotu ta soke waɗanda aka zaɓa a ƙarƙashin jami’iyyar PDP, bayan da ta ce jami’iyyar ba ta da zaɓaɓɓun shugabanni a jihar Filato a lokacin da aka gudanar da zaɓukan gama gari a shekara ta dubu biyu da ashirin da uku.

Continue Reading

Labarai

Zaɓen cike gurbi: Musa ya lashe kujerar Sanatan Yobe ta gabas

Published

on

Daga Ibraheem El-Tafseer

Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) ta bayyana ɗan takarar jam’iyyar All Progressive Congress (APC), Musa Mustapha a matsayin wanda ya lashe zaɓen cike gurbi na Sanatan Yobe ta Gabas da aka kammala.

Mataimakin shugaban jami’ar tarayya ta Gashua (FUGA), Ibrahim Ahmed Jajere, wanda shi ne jami’in zaɓe na zaɓen, ya bayyana Mustapha a matsayin wanda ya lashe zaɓen bayan an kammala ƙidaya ƙuri’u a cibiyar tattara ƙuri’u da ke Kwalejin gwamnatin tarayya (Federal Polytechnic Damaturu) ranar Lahadi.

Jajere ya ce ɗan takarar jam’iyyar APC ya samu ƙuri’u dubu 68,778 inda ya kayar da abokin hamayyarsa Aji Kolomi na jam’iyyar PDP wanda ya samu ƙuri’u dubu 18,878.

Jami’in zaɓen ya bayyana cewa, jimillar ƙuri’u dubu 90,949 da aka kaɗa, ƙuri’u dubu 88,771 yayin da ƙuri’u dubu 2,178 suka ɓaci.

KU KUMA KARANTA: Ɗan takarar Sanatan APC a Yobe ta gabas, ya yiwa al’ummomin Geidam da Yunusari alƙawarin morar romon dimokuraɗiyya 

“Ni, Mataimakin Farfesa Ibrahim Ahmed Jajere a nan na tabbatar da cewa ni ne Jami’in zaɓe na cike gurbi na takarar neman kujerar Sanatan Yobe ta Gabas na 2024 da aka gudanar a ranar 3 ga Fabrairu.

“An fafata tsakanin Musa Mustapha na APC ya samu ƙuri’u 68,778, Aji Kolomi na PDP ya samu ƙuri’u 18,878.

“Musa Mustapha na APC bayan ya cika dukkan sharuɗɗan doka an bayyana shi a matsayin wanda ya yi nasara kuma ya dawo zaɓaɓɓe,” in ji shi.

Mustapha wanda aka fi sani da Coolers tsohon kwamishinan kuɗi, sufuri da makamashi ne a jihar Yobe ya maye gurbin Sanata Ibrahim Geidam wanda ke riƙe da muƙamin ministan harkokin ‘yan sanda.

Ga sakamakon kamar haka;

Bursari
APC-9,466
PDP-2,752

Damaturu
APC: 11,941
PDP-6,693

Geidam
APC-6,621
PDP-2,310

Gujba
APC-11,529
PDP-3,037

Gulani
APC-12,516
PDP-2,198

Tarmuwa
APC-5,557
PDP-1,054

Yunusari
APC-11,148
PDP-834

Neptune Prime

Continue Reading

INEC

Yau ce ranar zaɓen cike gurbi da raba gardama a jihohi 26 na Najeriya

Published

on

Daga Maryam Umar Abdullahi

An hana zirga-zirgar ababen hawa har zuwa shida na yamma a jihohin da za a yi zaɓen.

A yau Asabar Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ke gudanar da zaɓukan raba-gardama da kuma na cike giɓi na kujerun majalisun tarayya da kuma na jihohi a 26 a ƙasar.

Za a gudanar da zaɓukan ne a ƙananan hukumomi 80 a faɗin Najeriya, domin cike gurbin wasu da suka rasu da ’yan majalisar da kotu ta cire ko kuma waɗanda suka sauka domin karɓar wasu muƙaman.

A cewar Shugaban INEC, Farfesa Mahmood Yakubu, za a yi zaɓen cike gurbi ne a jihohi tara daga cikin 26 domin zaɓar sanatoci biyu da ’yan majalisar wakilai na tarayya huɗu da kuma kujeru uku na majalisar jiha.

A zaɓukan gaba-ɗaya za a yi na kujerun sanatoci uku da kujerun majalisar wakilai 17 da kujeru 28 na majalisun jihohi a faɗin ƙananan hukumomi 80.

Wasu daga cikin fitattun kujerun da za a yi zaɓen nasu su ne, kujerar Honarabul Femi Gbajabiamila, wanda ya yi murabus ya karɓi mukamin Shugaban Ma’aikata na Fadar Shugaban ƙasa, da ta Sanata David da Sanata Ibrahim Geidam da Honarabul Bumi Tunji-ojo da Honarabul Tanko Sununu da suka yi murabus domin karɓar muƙamin ministoci.

Akwai kuma kujerar majalisar wakilai ta Honarabul Isma’ila Maihanchi, daga Taraba, wanda ya rasu tun kafin rantsar da shi da kuma Honarabul Abdulƙadir Danbuga daga Sokoto wanda ya rasu a watan Oktoba na 2023.

KU KUMA KARANTA:Babban jami’in MƊD ya damu da yiwuwar kai farmakin da Isra’ila ke yi a Rafah

Jihohin da za a yi zaɓukan sun haɗa da Ebonyi, da Yobe, da Kebbi, da Legas, da Ondo, da Taraba, da Benuwe, da Borno, da Kaduna, da Filato, da Akwa Ibom, da Anambara, da Kuros Riba, da Delta, da Enugu, da Jigawa, da Katsina, da Adamawa, da Bauchi, da Bayelsa, da Kano, da Nasarawa, da Neja, da Oyo, da Sokoto, da kuma Zamfara.

Dangane da zaɓukan Babban Sufeton ‘Yan-sanda Kayode Egbetokun, ya bayar da umarnin hana zirga-zirgar ababen hawa daga ƙarfe 12 na dare zuwa shida na yamma a jihohin da za a yi zaɓen.

Wannan dai na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da jami’in hulɗa da al’umma na rundunar ’yan sandan Najeriya, Olumuyi Adejobi ya fitar tun a ranar Alhamis.

Sanarwar ta ce dokar taƙaita zirga-zirgar ba ta shafi masu muhimman ayyuka ba, kamar ma’aikatan kashe gobara da ‘yan jarida da jami’an INEC da likitoci da masu sanya ido a zaɓukan.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like