Connect with us

Labarai

Zaɓen cike gurbi: Musa ya lashe kujerar Sanatan Yobe ta gabas

Published

on

Daga Ibraheem El-Tafseer

Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) ta bayyana ɗan takarar jam’iyyar All Progressive Congress (APC), Musa Mustapha a matsayin wanda ya lashe zaɓen cike gurbi na Sanatan Yobe ta Gabas da aka kammala.

Mataimakin shugaban jami’ar tarayya ta Gashua (FUGA), Ibrahim Ahmed Jajere, wanda shi ne jami’in zaɓe na zaɓen, ya bayyana Mustapha a matsayin wanda ya lashe zaɓen bayan an kammala ƙidaya ƙuri’u a cibiyar tattara ƙuri’u da ke Kwalejin gwamnatin tarayya (Federal Polytechnic Damaturu) ranar Lahadi.

Jajere ya ce ɗan takarar jam’iyyar APC ya samu ƙuri’u dubu 68,778 inda ya kayar da abokin hamayyarsa Aji Kolomi na jam’iyyar PDP wanda ya samu ƙuri’u dubu 18,878.

Jami’in zaɓen ya bayyana cewa, jimillar ƙuri’u dubu 90,949 da aka kaɗa, ƙuri’u dubu 88,771 yayin da ƙuri’u dubu 2,178 suka ɓaci.

KU KUMA KARANTA: Ɗan takarar Sanatan APC a Yobe ta gabas, ya yiwa al’ummomin Geidam da Yunusari alƙawarin morar romon dimokuraɗiyya 

“Ni, Mataimakin Farfesa Ibrahim Ahmed Jajere a nan na tabbatar da cewa ni ne Jami’in zaɓe na cike gurbi na takarar neman kujerar Sanatan Yobe ta Gabas na 2024 da aka gudanar a ranar 3 ga Fabrairu.

“An fafata tsakanin Musa Mustapha na APC ya samu ƙuri’u 68,778, Aji Kolomi na PDP ya samu ƙuri’u 18,878.

“Musa Mustapha na APC bayan ya cika dukkan sharuɗɗan doka an bayyana shi a matsayin wanda ya yi nasara kuma ya dawo zaɓaɓɓe,” in ji shi.

Mustapha wanda aka fi sani da Coolers tsohon kwamishinan kuɗi, sufuri da makamashi ne a jihar Yobe ya maye gurbin Sanata Ibrahim Geidam wanda ke riƙe da muƙamin ministan harkokin ‘yan sanda.

Ga sakamakon kamar haka;

Bursari
APC-9,466
PDP-2,752

Damaturu
APC: 11,941
PDP-6,693

Geidam
APC-6,621
PDP-2,310

Gujba
APC-11,529
PDP-3,037

Gulani
APC-12,516
PDP-2,198

Tarmuwa
APC-5,557
PDP-1,054

Yunusari
APC-11,148
PDP-834

Neptune Prime

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like