Connect with us

'Yansanda

Yan sanda sun ceto yarinyar da ƙanwar mahaifiyarta ta kulle a Filato

Published

on

Rundunar ‘yan sandan jihar Filato ta ceto wata yarinya ‘yar shekara 17 da ƙanwar babarta ta kulle a garin Jos babban birnin jihar.

Kamar yadda kamfanin dullancin labarai na Najeriya wato NAN ya ruwaito, cewa jami’ar hukumar kare haƙƙin bil’adama ta ƙasa (NHRC) a jihar Filato, Grace Pam, ta ce an ceto yarinyar ne a unguwar Rikkos da ke ƙaramar hukumar Jos ta Arewa.

Pam ta ce an kawo yarinyar ne domin ta zauna tare da ƙanwar mahaifiyarta bayan kakarta da ke kula da ita ta fara jinya.

“Hukumar ta samu labari daga wani da yayi ƙorafin da ba a bayyana sunansa ba cewa ’yar uwar ta kulle yarinyar a barandar gidan,” inji ta.

Ta kasance tare da kakarta kafin ta zo gidan innar ta saboda kakar ta yi rashin lafiya kuma ba za ta iya ci gaba da kula da ita ba.

Mai ƙarar ya yi ƙorafin cewa innar ta yi tafiyar kusan mako guda kuma ta bar yarinyar babu abinci.
“Bincike ya nuna cewa lallai yarinyar tana fama da rashin abinci kuma tana da tabo a hannunta, wuyanta, da sauran sassan jikinta.

” Tabon ya samo asali ne daga dukan da ake yi mata ba ƙakƙautawa daga wajen innar.

“An kai rahoton lamarin ga ‘yan sanda inda aka ɗauki bayanin goggon bayan dawowarta daga tafiyar ta.

“An samar wa yarinyar wurin kwana na wucin gadi har sai ta warke.

“Mun kuma gano cewa yarinyar marainiya ce, ba a taba barin ta fita ba, amma an kulle ta a gida, ba a ba ta abinci ba.

“Ɗaya daga cikin abokan aikinmu ne ya kai ta asibiti don tabbatar da an bata kulawar da ta dace” inji shi.

Shugabar hukumar ta NHCR a jihar Filato ta bayyana damuwarsa kan yadda ake samun yawaitar cin zarafin ƙananan yara, inda ya ƙara da cewa, “a yayin da muke magana, akwai wata yarinya ‘yar shekara tara da ta zo ta zauna da goggonta watanni biyu da suka wuce, da ita ma aka ci zarafinta.

“Dole ne muka kubutar da ita a ranar Alhamis daga hannun innarta; ta yi mata dukan tsiya, amma alhamdulillahi, ba ta samu makanta ba sai dai ta samu rauni a ido”.

Ta ƙara da cewa. “Mun kai ta asibiti a ranar Juma’, ta samu da tabo a jikinta sakamakon duka da aka yi mata.

“Lokacin da ma’aikatanmu suka je wurin, an kulle ta a wani gidan kwano da kwano inda goggon ke ajiye awakinta.

“Yarinyar tana fatan komawa wurin iyayenta.” Inji ta.

2 Comments

2 Comments

  1. Pingback: Matar da mijinta ya ɗaure a ɗaki ta rasu a Kano | Neptune Prime Hausa

  2. Pingback: An ceto ɗalibar da tayi yunƙurin kashe kanta | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

'Yansanda

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

Published

on

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

Rundunar ’yan sandan Najeriya ta tube wa wasu jami’an ta biyar kaki sakamakon zargin su da karɓar cin hancin kuɗi kimanin Naira miliyan uku.

Mataimakin Shugaban ’yan Sanda mai kula da Shiyya ta shida ta da ke Jihar Kuros Riba, Jonathan Towuru, ya sanar a Kalaba cewa ’yan sandan sun kwace kuɗin ne da bakin bindiga a hannun wani mai abin hawa.

A makon jiya ne aka zargi jami’an da ƙwayar kuɗin da bakin bindiga a hannun wani mutum da rundunar ta sakaya sunansa.

Yanzu haka waɗanda ake zargin an tuɓe masu kaki amma ana tsare da su ana bincike, da zarar an same su da laifi kotu za a turasu ta yanke masu hukuncin da ya dace.

KU KUMA KARANTA: ’Yan sanda za su tantance ’yan banga a Yobe

Mataimakin shugaban ’yan sandan ya ce waɗanda ake zargin su da karɓar cin hancin kuɗi Naira milyan uku daga wannun wani.

Ko a kwanan baya irin haka ta taba faruwa a kan babbar hanyar Kalaba zuwa Ikom inda aka kama wasu ’yan sanda kan karbar na goro.

Tafiya a kan hanyar na yawan zargin ’yan sanda da kula da shingen bincike a kan hanyar da yawan tatsar su kuɗi.

Continue Reading

'Yansanda

‘Yan sanda sun kama mutum 2 da ake zargin sace mahaifiyar Rarara

Published

on

Yan sanda sun kama mutum 2 da ake zargin sace mahaifiyar Rarara

‘Yan sanda sun kama mutum 2 da ake zargin sace mahaifiyar Rarara

Rundunar ’yan sandan Jihar Katsina ta sanar da cafke wasu mutum biyu bisa zargin hannu a garkuwa da mahaifiyar fitaccen mawaƙin siyasar nan, Dauda Kahutu Rarara.

Mai magana da yawun rundunar a Katsina, ASP Abubakar Sadiq Aliyu ya ce “muna tsare da mutum biyu kan lamarin, muna ci gaba da bincike.”

Tun farko, Kwamishinan tsaro na Jihar Katsina, Nasiru Mu’azu ya ce an sace dattijuwar ce a daren Juma’a a ƙauyen Kahutu da ke Karamar Hukumar Ɗanja.

Mu’azu ya ce waɗanda suka sace matar sun yi hakan ta hanyar bi ta bayan gida, inda suka sace ta ba tare da jami’an da ke tsaron gidan sun sani ba.

Ya kuma bayyana cewa tuni aka tura jami’an tsaro waɗanda suka bazama cikin dazuka domin bin sawun ’yan bindigar.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan bindiga sun yi garkuwa da mahaifiyar mawaƙi Rarara

Neptune Prime Hausa ta ruwaito shaidu a kauyen sun ce da misalin karfe daya na dare ne dandazon ’yan bindiga suka kutsa gidan dattijuwar suka yi awon gaba da ita.

“A kafa suka zo, ba su yi harbi ba a lokacin da suka ka yi awon gaba da ita cikin ’yan mintoci.

“Dattijuwar ba ta bijire musu ba a lokacin da suka memi ta biyo su.

“Duk da cewa ’yan bindigar sun samu wasu mutane a gidan, amma mahaifiyar Rarara kaɗai suka ɗauka.

“Babu wani yunƙuri da aka yi na tunkarar ’yan bindigar a lokacin da suke tafiya da ita saboda bindigogin da suke ɗauke da su,” in ji wani mazaunin ƙauyen na Kahutu.
Ya ce, “Watakila maharan sun bar baburansu ne daga nesa suka tako zuwa cikin ƙauyen a kafa.

“Muna rokon Allah Ya kuɓutar da ita cikin koshin lafiya domin tana taimaka mana sosai a wannan ƙauyen.

“Danta Rarara mai yawan taimakon al’umma ne, kuma ya kawo mana abubuwan ci gaba sosai a garinmu,” in ji shi.

Continue Reading

'Yansanda

‘Yan sanda sun kama kawali na ’yan bindiga

Published

on

'Yan sanda sun kama kawali na ’yan bindiga

‘Yan sanda sun kama kawali na ’yan bindiga

Daga Muhammad Kukuri 

Wani wanda yake kai wa ’yan bindiga karuwai domin yin lalata da su ya shiga hannun jami’an tsaro.

’Yan sanda sun bayyana cewa kawalin ya kuma ƙware wajen yin safarar makamai ga ƙungiyar jagoran ’yan bindiga mai suna Arɗo, wanda ake nema ruwa a jallo a yankin Kagarko da ke Jihar Kaduna.

An kuma gano cewa mutumin wanda yake harkar hada-hadar tura kuɗi ta PoS, shi ke kai wa iyalan ’yan bindiga kuɗaɗe a yankin na Kagarko.

Dubun kawalin ta cika ne a yayin wani samamen haɗin gwiwa da ’yan sanda suka gudanar a yankin.

Kwamishinan ’Yan Sandan Birnin Tarayya, ya sanar ranar Talata cewa wanda ake zargin ya shaida musu cewa shi ke tsara yadda ake kai wa ’yan bindiga karuwai da miyagun ƙwayoyi da ma’aikatan lafiya a duk lokacin da suke buƙata.

KU KUMA KARANTA: Ƴan sanda a Kano sun kai mutanen da ake zargi da sayar da dala ba bisa ƙa’ida ba kotu

“Ya kuma amsa cewa yana yin dakon kuɗi tare da rabawa ga iyalan ’yan bindiga.

“A cewarsa, kuɗaɗen da ya raba wa iyalan ’yan bindiga sun haura Naira miliyan ashirin,” in ji kwamishinan ’yan sandan.

Igwe ya ce wanda ake zargin ya tabbatar musu cewa ’yan bindigar da ke ƙarƙashin Ardo sun kai 15 kowannensu da bindiga ƙirar AK-47.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like