Connect with us

'Yan bindiga

’Yan bindiga sun sace mata biyu ’yan gida ɗaya a Abuja

Published

on

Ana fargabar cewa ’yan bindiga sun sace wasu ’yan mata biyu ’yan gida yayin wani hari da suka kai kauyen Guite da ke gundumar Chikakore ta ƙaramar hukumar Kubwa da ke Abuja.

Aminiya ta ruwaito cewa, ’yan bindigar bayan sace ’yan mata masu shekaru 14 da 16 sun tsere cikin wani jeji wanda ya yi iyaka da ƙauyen da wasu ƙauyuka maƙwabta.

Bayan kwashe ‘yan matan ne kuma ‘yan bindigar suka ranta a na kare inda suka shiga daji wanda ya haɗa ƙauyen da wasu ƙauyukan masu maƙwabtaka.

Wani mazaunin ƙauyen wanda a buƙaci a sakaya sunansa, ya shaida wa wakilinmu cewa lamarin ya faru ne a ranar Lahadin da ta gabata.

A cewar majiyar, “’yan bindigar sun kutsa gidan ne ba tare da harbi irin na kan-mai-uwa-da-wabi ba kamar yadda suka saba sannan suka kama ’yan matan guda biyu.”

KU KUMA KARANTA: ‘Yan bindiga sanye da hijabi sun afka wa ofishin ‘yan sanda a Katsina

Sai dai an yi rashin sa’a a ƙoƙarin jin ta bakin mai magana da yawun rundunar ’yan sandan Abuja SP Adeh Josephine sakamakon rashin amsa ƙiran wayar da aka yi mata.

Wannan ne dai karo na biyu a ƙasa da wata guda da ’yan bindiga ke yin garkuwa da ’yan mata ’yan uwan juna a babban birnin na tarayya.

Neptune Prime Hausa ta ruwaito yadda a makonnin da suka gabata wasu ‘yan bindiga suka sace mutane daga rukunin gidaje na Sagwari da ke unguwar Dutsen-Alhaji a Karamar Hukumar Bwari da ke Abuja.

Masu garkuwa da mutanen sun kashe huɗu daga cikinsu, ciki har da wata ɗalibar jami’ar Ahmadu Bello, Nabeeha Al-Kadriyar, da kuma Folashade Ariyo mai shekara 13.

An sace Nabeeha ce tare da ’yan uwanta mata biyar da mahaifainsu daga gidansu da ke unguwar Zuma 1 a wajen garin Bwari a ranar 2 ga watan Janairu.

Matsalar tsaro dai na ƙara ta’azzara a birnin na Abuja, lamarin da ke ƙara jefa fargaba a zukatan mazauna birnin.

To sai dai a baya rundunar ’yan sandan birnin ta sha cewa tana iya bakin ƙoƙarinta wajen ganin su daƙile matsalar.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

'Yan bindiga

‘Yan bindiga sun kashe malamin jami’a a Katsina, sun sace ‘ya’yansa

Published

on

'Yan bindiga sun kashe malamin jami'a a Katsina, sun sace 'ya'yansa

‘Yan bindiga sun kashe malamin jami’a a Katsina, sun sace ‘ya’yansa

Rahotanni daga Jihar Katsina  na cewa ‘yan bindiga sun kashe wani malamin Jami’ar Tarayya ta Dutsinma.

Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne a ranar Talata da tsakar dare da misalin ƙarfe 1:30 inda ‘yan bindigar suka afka gidan Dakta Tiri Gyan da ke Yarima Quarters a Ƙaramar Hukumar Dutsinma.
Mai magana da yawun ‘yan sandan  reshen Katsina Abubakar Sadiq ya tabbatar wa kafar watsa labarai ta Channels  da kisan malamin.

Waɗanda suka shaida lamarin sun bayyana cewa ‘yan bindigar sun afka gidan malamin jami’ar da makamai daban-daban inda suka yi ta harbi domin tsorata mazauna rukunin gidajen.

Sun kuma bayyana cewa ɓarayin sun sace yara biyu na Dakta Gyan a lokacin da suka kai harin.

KU KUMA KARANTA: ’Yan bindiga sun sace Hakimi da manoma 2 a Kaduna

Kashe malamin na zuwa ne mako guda bayan kashe mataimakin Shugaban Jami’ar Usman Ɗanfodiyo da ke Sokoto Farfesa Yusuf Saidu.

An kashe shi a lokacin da yake hanyarsa ta zuwa Kaduna daga Sokoto.

Continue Reading

'Yan bindiga

Muna ƙoƙarin kuɓutar da ɗaliban jami’ar da ‘yan bindiga suka sace – Gwamnatin Kogi

Published

on

‘Yan bindigar dai sun aukawa jami’ar kimiyya da fasaha ne dake garin Osara a ƙaramar hukumar Adabi a jihar Kogi inda bayan jikkata wasu ɗaliban, sannan suka yi garkuwa da wasu kimanin 57.

Malam Ɗan Asabe wani mazaunin jihar Kogi yace ‘yan bindigar sun haura cikin jami’ar ne ta baya suka dinga harbin kan mai uwa da wabi kamar yadda ya yiwa wakilin Muryar Amurka bayani ta wayar salula.

Tuni dai Gwamnatin jihar Kogin ta yi Allah wadai da wannan hari tare da nuna takaicinta akan lamarin.

Kwamishinan Labarai na jihar Kogin, Kensly Fanwo, yace, kawo yanzu ba su tantance adadin ɗaliban da ‘yan bindigar suka sace ba, amma sun haɗa hannu da jami’an tsaro domin ganin an kuɓuta da ɗaliban cikin ƙoshin lafiya.

KU KUMA KARANTA:’Yan bindiga sun sace ɗalibai a Jami’ar Jihar Kogi

Ya ƙara da cewa, a lokacin da gwamnatin jihar ta samu labarin ta yi ƙoƙarin jibga jami’an tsaro a wannan yanki domin samun nasarar kuɓutar da ɗaliban da aka sace.

A wata sanarwa daga kakakin ‘yan sandan jihar Kogin, Wilyans Aya, ya ce kwamishinan ‘yan sandan ya ƙara tura jami’an tsaro na musamman domin samun nasarar kuɓutar da ɗaliban.

Garkuwa da ɗaliban makaranta dai na ci gaba da ɗaukar hankali a Nijeriya, al’amarin da masana suka ce babbar barazana ce a ɓangaren Ilimi a ƙasar.

Continue Reading

'Yan bindiga

An sace limaman coci 6 a Anambara

Published

on

Rahotanni daga Najeriya na cewa ‘yan bindiga sun yi garkuwa da wasu limaman Coci shida yayin da suke kan hanyarsu ta zuwa birnin Awka na jihar Anambara a kudu maso gabashin Najeriya.

Bayanai sun yi nuni da cewa ‘yan bindigar sun sace Archbishop Uka Uka na Mujami’ar Brotherhood of the Cross and Star, (BCS) da matarsa Anne Osim da ɗansu Ronald Uka Osim.

Sauran limaman Cocin sun haɗa da Azuka Ochu, Moses Okafor da Anderson Akwazie a cewar jaridar Daily Trust.

Jaridar Daily Post ta yanar gizo ta ruwaito cewa mutanen na hanyarsu ta zuwa Awka ne daga jihar Abiya don gudanar da ayyukan wa’azi a lokacin da lamarin ya faru.

Al’amarin ya faru ne a ranar 1 ga watan nan na Mayu kamar yadda rahotanni suka nuna.

KU KUMA KARANTA:An halaka direba da sace mutum 2 a hanyar Abuja

“Mun damu matuƙa, amma muna da tabbacin cewa Ubangijin da suke bautawa zai taimaka musu.” Jaridar ta Daily Post ta ruwaito wani Limami a Cocin ta BCS, Bishop Denis Onuoha yana cewa.

Sai dai rundunar ‘yan sandan jihar Anambara, ta ce ba ta da masaniyar aukuwar wannan al’amari.

“Ba mu da wasu bayanai da suka nuna aukuwar wannan al’amari a jihar Anambara.” Wata sanarwa da rundunar ta wallafa a shafinta na Facebook ta ce a ranar Asabar ɗauke da sa hannun Kakakinta SP Tochukwu Ikenga.

Sanarwar ta ƙara da cewa, “muna ƙira ga jama’a da su taimaka mana da bayanai kan wannan al’amari idan har ya faru, hakan zai ba mu dama mu ƙaddamar da bincike.”

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like