Connect with us

Labarai

‘Yan bindiga sun kai hari fadar Sarkin Minna, sun harbe masu gadi, sun kwashe kuɗi

Published

on

Wasu da ake zargin ‘yan fashi da makami ne a ranar talata sun kai hari fadar Sarkin Minna, Umar Faruk Bahago, inda suka yi awon gaba da wasu kuɗaɗe da ba a tantance adadinsu ba.

Jaridar DAILY NIGERIAN ta ruwaito cewa ‘yan fashi da makami sun bi sawun jami’in, wanda ke dawowa daga bankin kasuwanci inda ya cire kuɗi.

Da yake tabbatar da faruwar lamarin, sakataren masarautar Minna, Garba Musa, ya ce jami’an tsaron fadar guda biyu da suka samu raunuka harbin bindiga suna karɓar magani a babban asibitin Minna.

“Muna cikin gida tare da Mai Martaba Sarki, sai muka fara jin ƙara mai nauyi. Da farko, muna tsammanin yara ne kawai suke wasa.

Amma nan take muka ji mutane suna kururuwa ‘ɓarayi ne; ɓarayi ne’.

KU KUMA KARANTA : ‘Yan bindiga sun harbe ɗan sanda a Ibadan

Don haka na yi gaggawar fitowa na tarar a zahiri harin fashi da makami ne,” in ji Malam Musa.

“Sun harbe biyu daga cikin masu gadin fadar da ke ƙoƙarin daƙile harin. Sai dai kash an harbi ɗaya a cinyarsa yayin da ɗaya kuma aka harbe shi a ƙirji. Nan take aka garzaya da su babban asibiti.”

Ya ce ‘yan bindigar sun bi ta ƙofar gida ta biyu inda suka samu shiga inda sarkin yake zaune. “Sun yi tirela da hanya ta ƙofa ta biyu, amma ba su haura sama inda sarki yake zaune ba.

Wataƙila sun yi tunanin idan suka ci gaba zuwa wurin, za a iya kama su.

Amma sun yi nasarar kwashe kuɗaɗen ne saboda suna harbin iska har sai da suka samu hanya,” inji shi.

Malam Musa ya kuma tabbatar da cewa kuɗaɗen da aka sace na masarautar ne.

Ya ƙara da cewa an sanar da ‘yan sanda lamarin, kuma sun yi alkawarin za su ɗauki matakin kamo masu laifin.

2 Comments

2 Comments

  1. Pingback: ‘Yan bindiga sun kashe mutane tara tare da ƙona gidaje shida a yankin Filato | Neptune Prime Hausa

  2. Pingback: ‘Yan bindiga sun kashe mutane tara tare da ƙona gidaje shida a yankin Filato - LEGEND FM DAURA

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like