Connect with us

Boko Haram

‘Yan Ansaru nata ɗaura aure da ‘yan mata a Jihar Kaduna

Published

on

Yan ƙungiyar Ansaru na ɗaura aure tsakanin mayaƙanta da ‘yan matan yankin Birnin-Gwari a Jihar Kaduna.

BBC ta ruwaito cewa irin wannan lamari ya faru ne a garin Tsohuwar Kuyallo, inda wasu ‘ya’yan ƙungiyar suka angwance da ‘yan matan garin a ranar Talata.

Wani mazaunin yankin Birnin Gwari ya tabbatar wa BBC da ɗaurin auren, inda ya ce ba sabon abu ba ne a yankin.

Ya ƙara da cewa ko a watanni kimanin biyu da suka gabata mayaƙan ƙungiyar sun haɗa aure da wasu ‘yan mata biyu a yankin.

BBC ta tuntuɓi rundunar ‘yan sandan Nijeriya reshen Jihar Kaduna game da wannan lamari, inda ta ce tana gudanar da bincike a kai.

Sai dai masana harkokin tsaro kamar Muhammad Kabir Isa na Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zaria, na ganin sakacin gwamnatin Nijeriya ne ta fuskar tsaron ya sa ƙungiyar ke amfani da irin waɗannan hanyoyi domin samun shiga tsakanin al’umma, har abin ya kai ga haɗa zuri’a.

“Yanzu idan suka yi aure cikin jama’a, yaran gidan ko mazan da ke ciki sun zama nasu, waɗannan duk dabaru ne na samun mabiya da mutanen da za su dauki akida da ra’ayoyinsu,” in ji Muhammad Kabir.

Ya bayyana cewa kulawar da gwamnati ta gaza bayarwa ne har ya sa ƙungiyoyi kamar Ansaru ke shiga cikin al’ummomi domin ba su tallafi domin jawo ra’ayinsu.

Yankin Birnin Gwari na Jihar Kaduna na daga cikin yankunan da ƙungiyoyin tayar ƙayar baya suka addaba.

Yanki ne da a tsawon shekaru ‘yan fashin daji ke kai hare-hare a garuruwa da kuma kan matafiya a hanyoyi, inda suke kashewa ko garkuwa da su.

Sai dai a baya-bayan nan yankin ya ƙara shiga tasku, bayan da rahotanni ke ta nuna cewa ƙungiyar ta Ansaru ta samu gindin zama a nan.

An riƙa samun bayanai kan yadda suke iko da wasu yankunan na Birnin Gwari, har ta kai ga suke da wuƙa da nama kan abubuwan da ke faruwa a wasu garuruwan.

Kamar yadda binciken cibiyar Nazari kan tsaro ta ISS ya nuna, Ansaru ta kafu ne a wasu yankunan Arewacin Nijeriya shekaru 10 da suka wuce.

Kuma ta samu ne bayan ballewar wasu ‘ya’yan babbar ƙungiyar Boko Haram, a dalilin rashin jituwa tsakanin masu matsakaici da kuma masu tsattsauran ra’ayi.

Kuma tun daga lokacin take faɗaɗa hanyar ƙulla ƙawance da ƙungiyoyin ‘yan bindiga da garkuwa da mutane a yankin.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Boko Haram

An tabbatar da mutuwar masu juna biyu a cikin harin da aka kai a Borno

Published

on

An tabbatar da mutuwar masu juna biyu a cikin harin da aka kai a Borno

An tabbatar da mutuwar masu juna biyu a cikin harin da aka kai a Borno

An kasha aƙalla mutane 18, yayin da wasu 30 suka jikkata bayan wasu jerin hare-haren da ake zargin wasu mata ‘yan ƙunar baƙin wake ne suka kai a jihar Borno a jiya Asabar, in ji shugaban hukumar bayar da agajin gaggawa ta yankin.

Borno dai na cikin shekaru 15 na hare-haren masu iƙirarin kishin Islama wanda ya yi sanadiyar mutuwar dubban mutane tare da raba wasu miliyoyi da humallan su.

Duk da cewa sojojin Najeriya sun rage ƙarfin mayaƙan, amma har yanzu suna kai munanan hare-hare kan fararen hula da kuma wuraren tsaro.

KU KUMA KARANTA:Gobara ta tashi a matatar man Ɗangote

Barkindo Saidu, shine babban Daraktan Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Borno, ya ce wasu da ake zargin ‘yan ƙunar baƙin wake ne suka kai hari daban-daban a wajen bikin aure da jana’iza da kuma asibiti, inda suka kashe mutane tare da jikkata wasu da dama a garin Gwoza.

Saidu ya ce an tabbatar da mutuwar mutum 18, adadin da ya haɗa da ƙananan yara da manya da ma mata masu juna biyu.

Sai dai babu wata ƙungiyar ko wani mutun da ya ɗauki alhakin kai wannan harin.

Boko Haram da ISWAP da ta ɓalle kanta, su ne ƙungiyoyin ‘yan bindiga da suka fi yawan gudanar da ayyukan su a jihar Borno, wani babban yanki na karkara mai girman gaske.

Continue Reading

Boko Haram

Boko Haram sun kashe manoma 15 a jihar Borno

Published

on

Wasu da ake zargin ‘yan ƙungiyar Boko Haram ne sun kashe aƙalla mutane 15 a hare-haren da suka kai kan wasu ƙauyuka biyu a ƙaramar hukumar Jere ta jihar Borno.

Kamar yadda rahoton Daily Trust ta ruwaito, ‘yan ta’addan sun kai farmaki ƙauyen Ƙofa ne da tsakar dare inda suka fara harbe-harbe ba da daɗewa ba, wanda har zuwa safiyar Juma’a.

An tattaro cewa maharan sun kuma kai hari a ƙauyukan Molai Kura da Molai Gana inda suka yi ta yanka mutane da ba a tantance adadinsu ba.

KU KUMA KARANTA: Yadda ‘yan Boko Haram suka yiwa masunta 29 kisan gilla, suka jikkata 9 a Gamborun Ngala

Lamarin dai ya sa mazauna yankin da dama sun ƙauracewa gidajensu zuwa wani daji da ke kusa.

Wani jigo a ƙungiyar ’yan banga, Bukar Ali-Musty, ya shaida wa jaridar cewa manoman na aikin gonakinsu ne a kusa da Molai, da ke wajen birnin Maiduguri, a ranar Alhamis ɗin da ta gabata, inda ‘yan tada ƙayar bayan suka kai musu hari suka sare kawunansu.

“Aƙalla gawarwaki 15 ne aka kwashe a safiyar yau, an kai hare-haren ne jiya (Alhamis).

“An sare kan manoma bakwai a lokacin da suke aikin gonakinsu, sannan maharan sun kuma yanka wuya ga wasu fararen hula takwas da ba su da illa a gidajensu,” in ji shi.

Wani memba a ƙungiyar ‘civilian JTF’ da ke cikin tawagar da aka kwashe, ya nuna damuwarsa kan hare-haren, yana mai cewa dole ne duk masu ruwa da tsaki su farka don ganin ba a ci gaba da faruwa ba.

“Abin takaici ne ci gaba idan aka yi la’akari da ci gaban da muka samu a cikin watanni ba tare da an kai wa al’umma hari ba.

“Ina can da safe. Ba zan iya tunanin ganin an yanka ’yan uwana kamar rago ba.

Dukkanin gawarwakin da muka ƙwato an same su ne a cikin kwance cikin jini, kuma ina ganin dukkanmu muna buƙatar mu tashi tsaye domin tunkarar wannan maƙiyin zaman lafiya,” inji majiyar.

Continue Reading

Boko Haram

ISWAP ta kashe mutane uku da jikkata sojoji takwas a Borno

Published

on

Aƙalla ‘yan gudun hijira guda uku ne aka kashe tare kuma da jikkata wasu 13 ciki har da sojoji guda takwas a wasu mabambantan hare-hare da ƙungiyar ISWAP ta kai ƙaramar hukumar Damboa na jihar Borno.

An ruwaito cewa lamarin ya faru ne lokacin da ‘yan gudun hijira guda huɗu da ke zama a sansanin Lowcost a Damboa suka fita domin neman itacen hura wuta lokacin da mayaƙan suka buɗe musu wuta, inda suka kashe uku nan take yayin da sauran mutane kuma suka tsere da raunuka.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa tun da farko ISWAP ɗin sun jikkata wasu sojoji da kuma fararen hula yayin wani hari da suka kai yankin Talala a ranar Talata duk a Damboa.

Wata majiyar tsaro ta tabbatar da cewa sojoji sun kashe mayaƙan na ISWAP da dama a wani hari da suka kai musu.
Majiyar ta ce wani jrgin sama na sojoji ya je Damboa a jiya Alhamis, inda ta ɗebo sojoji da suka jikkata zuwa Maiduguri domin yi musu magani.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like