Connect with us

Kudanci

Yadda ‘yar shekara 13 ta haihu bayan tsoho mai shekaru 75 da ke riƙonta ya mata ciki

Published

on

Ma’aikatar mata da walwalar jama’a ta jihar Anambra ta ƙuɓutar da wata yarinya ‘yar shekara 13 da ta haihu bayan da aka yi zargin mai kula da ita, Mista Sunday Muoghalu ya yi mata ciki.

A ƙarshen makon da ya gabata ne, labarin haihuwar jaririn ya bazu a shafukan sada zumunta, inda ya nuna mahaifiyar matashiyar tare da jaririnta a wani asibiti da ke Adazi-Nnukwu a ƙaramar hukumar Anaocha ta jihar Anambra.

An tsare ta ne saboda rashin biyan kuɗin asibiti.

Lamarin da ya sa gwamnatin jihar ta nemi wata tawagar ma’aikatar mata ta kuɓutar da ita kuma suka ajiye ta a wajen su.

Mai magana da yawun ma’aikatar, Chidimma Ikeanyionwu, a ranar litinin, ya ce an kama Muoghalu a ranar lahadi kuma aka mika shi ga ‘yan sanda.

Matashiyar ‘yar shekara 13 da ta haihu, ta ce ta fito daga jihar Akwa Ibom, yayin da iyayenta suke zauna a Agulu, jihar Anambra.

Ta ce, “Matar Mista Muoghalu ana kiranta Madam Ghana. Hakan ya faru ne lokacin da Madam Ghana ta yi tafiya zuwa ƙauyen su.

KU KUMA KARANTA:An kama likita kan zargin lalata da ‘yar shekara 15, ‘yar uwar matarsa

“Ba ni kaɗai ya yi wa ba, akwai wata yarinya ‘yar shekara bakwai; Mista Muoghalu ya kasance yana lalata da ita ma.

“Wannan ya faru ne lokacin da na fara ganin hailata, sai ya fara tilasta ni na kwana da shi. Na taɓa gaya wa Madam Ghana game da lamarin, kuma ta gargaɗi mijinta, amma da abin ya ci gaba, sai na kasa yin komai.”

Kwamishiniyar kula da harkokin mata da yara ta jihar, Misis Ify Obinabo, ta bayyana cewa, nan ba da jimawa ba za a gurfanar da mai laifin.

Ta ce, “Idan wanda ake zargin yana da’awar cewa ba shi da laifi, za mu ci gaba da bincike har sai mun gano wanda ke da hannu a ciki.

“Gaskiyar lamarin yayi muni, wani yayi lalata da karamar yarinyar,ya sa ta zama uwa, hakan ba daidai ba ne.

“Don haka, duk wanda ke da hannu a laifin, dole ne a gabatar da shi kuma wannan gwamnati ta himmatu wajen yin hakan.”

Wanda ake zargin, Muoghalu, ya ce shi ne ke da alhakin daukar cikin.
Ɗan shekaru 75 ya bayyana cewa yana wasa ne kawai da yarinyar, bai yi niyyar yi mata ciki ba.

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, DSP Tochukwu Ikenga, ya ce ana ci gaba da gudanar da bincike.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Hatsari

Jirgin sama mai sauƙar ungulu ya faɗo a Legas

Published

on

Wani jirgin sama mai sauƙar ungulu ya yi hatsari a yankin Ikeja da ke Jihar Legas a kudancin Najeriya.

Wani jami’in hukumar ba da agajin gaggawa ta Legas ya ce jirgin ya kama da wuta jim kaɗan bayan rikitowarsa da tsakar ranar Talata a kusa da filin jirgin sama na Murtala Muhammad.

KALLI CIKAKKEN BIDIYON ANAN:

Hukumar agajin gaggawa ta Najeriya, ‘National Emergency Management Agency’ (NEMA), ta ce mutum huɗu ne ke cikin jirgin kuma an ceto su da ransu.
Jami’in NEMA mai kula da sashen kudu maso yamma, Ibrahim Farinloye, ya ce ba su kai ga gano mamallakin jirgin ba ya zuwa lokacin haɗa wannan rahoton.

Lamarin ya faru ne shekara uku bayan wani jirgin Helikwafta mallakar kamfanin Quorom Aviation ya faɗo a yankin Opebi na Legas ɗin a watan Agustan 2020.

Continue Reading

'Yansanda

Da wane dalili ‘yan sanda suka lakaɗa wa ɗan Okada duka a Legas?

Published

on

Wani ɗan Okada, mai suna Alasan Usman matashi mai ƙoƙarin neman na kansa domin rufawa kansa da ‘yan uwansa asiri.

A ranar jumu’a ‘yan sanda a jihar Legas suka tare shi suka ce ya kawo babur ɗinsa duk da dai bai san laifin da ya aikata ba, sai ya ƙi ya basu. Saboda ya ƙi basu suka masa duka sai kace ɓarawo sai da suka yi masa jina-jina yadda ba zai iya taɓuka komai ba, sannan suka tafi da mashin ɗinsa.

KU KUMA KARANTA: Ranar zuma ta duniya: Amfani da sirrikan dake tattare da zuma

Sai dai rahotanni sun tabbatar da cewa ‘yan Arewa mazauna Legas sun yi iya ƙoƙarinsu wajen ganin an baiwa wannan ɗan Okada haƙƙinsa.

Yanzu haka shugaban hukumar ‘yan sanda na jihar Legas ya ziyarce shi a inda yake jinya, sannan an mayar masa da kuɗin belin da aka karɓa na mashin ɗinsa an kuma ba shi guduwmawa mai yawan gaske, kuma yana nan yanzu haka yana samun sauƙi sosai a unguwar Abbatuwa dake Legas.

Continue Reading

Hatsari

Fashewar bututun ɗanyen mai yayi sanadiyar mutuwar mutane 12

Published

on

Rundunar ‘yan sandan jihar Rivers ta tabbatar da cewa mutane 12 ne suka mutu sakamakon fashewar magudanar mai a safiyar Juma’a a yankin Rumuekpe da ke ƙaramar hukumar Emoha a jihar.

Kakakin ’yan sandan jihar, SP Grace Iringe-Koko, ta bayyana haka a cikin wata sanarwa da ta fitar a Fatakwal, inda ta ce shaidar farko ya nuna waɗanda abin ya shafa na ɗiban ɗanyen man ne a lokacin da wurin ya kama wuta.

KU KUMA KARANTA: Kwastam ta kama tramadol ɗin naira miliyan 306 a Kaduna

Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) ya tattaro cewa, hakan ya afku ne a yayin da wata motar bas ɗauke da ɗanyen mai ta kama wuta, yayin da take barin wurin zuwa wata matatar mai ta haramtacciyar hanya a yankin.

“Ya zuwa yanzu mutane 12 ana kyautata zaton sun ƙone kurmus. Har yanzu ba a gama sanin sunayen waɗanda abin ya shafa ba,” inji ta.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like