Connect with us

'Yansanda

Yadda masu shirya garkuwa da mutane a yanar gizo suka yi wa wata mata fyaɗe

Published

on

Rundunar ‘yan sandan jihar Ribas ta fasa wata ƙungiyar ‘yan kasuwa ta yanar gizo, wadda suka ƙware wajen lallasa mata, garkuwa da mutane da fyade don karɓar kuɗin fansa.

Rundunar ‘yan sandan ta ce jami’an leken asirin ‘yan sandan sun kama wasu ‘yan kungiyar guda biyu a wurare daban-daban a ƙananan hukumomin Igwurita da Choba, Ikwerre da Obio/Akpor na jihar.

Mai magana da yawun rundunar, Grace Iringe-Koko, ta bayyana hakan a wata sanarwa da ta fitar a Fatakwal a ranar Laraba.

Iringe-Koko ta ce waɗanda ake zargi, Ikechi Promise da Darlington Obi, sun yaudari ‘yan matan ta hanyar neman ƙulla alaƙa tare da tattaunawa a wani shahararren dandalin sada zumunta na yanar gizo na Tinder.

Ta ce, sa’a ta suɓuce masu ne a lokacin da suka yi wa wata mata mai shekaru 28 da haihuwa irin wannan dabara, inda suka yi awon gaba da ita zuwa Chokocho da ke Fatakwal.

A cewar mai gabatar da rahoton ‘yan sandan, ɓarayin sun yi wa matar fyade, inda suka sace mata wayoyin iPhone guda biyu da wayar Samsung, sannan suka karɓi kuɗin fansa naira dubu 600 daga hannun ‘yan uwanta kafin su sake ta.

Sanarwar ta ci gaba da cewa, “Ayyukan sashen leken asiri na rundunar, a ranar 6 ga watan Janairun 2023, da misalin karfe 8:30 na dare, inda suka kama wani Ikechi Promise, mai shekaru 30, da Darlington Obi, mai shekaru 35.

“Kamen na su yana da nasaba ne da aika-aikar da suka yi kwanan nan a ranar 20 ga Disamba, 2022, da misalin karfe 7:45 na yamma, lokacin da wata mata mai shekara 28 ta kama hanyar zuwa Mahaɗar Kasuwar Igwurita, aka yi awon gaba da su zuwa bututun Chokocho.

“Waɗanda ake zargin sun amsa cewa tsarin da suke yi shi ne su jawo ‘yan mata ta hanyar tattaunawa kan manhajar Tinder don ƙulla dangantaka.

“ Shugaban kungiyar masu garkuwa da mutane, Promise Nwaobiri, mai shekaru 32, an bi sawunsa tare da kama shi a unguwar Choba, kusa da Fatakwal, a ranar 9 ga Janairu, 2023, da misalin karfe 1 na rana.

Kakakin ‘yan sandan ta ce ana samun ƙaruwar mace-mace ta hanyar yaudara da yin garkuwa da mutane ta kafafen sada zumunta.

Iringe-Koko ta shawarci ‘yan mata da su yi taka-tsan-tsan wajen ƙulla alaka a shafukan sada zumunta da za su buƙaci su yi balaguro don saduwa da mutanen da ba su sani ba.

1 Comment

1 Comment

  1. Pingback: Yadda masu shirya garkuwa da mutane a yanar gizo suka yi wa wata mata fyaɗe - LEGEND FM DAURA

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

'Yansanda

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

Published

on

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

Rundunar ’yan sandan Najeriya ta tube wa wasu jami’an ta biyar kaki sakamakon zargin su da karɓar cin hancin kuɗi kimanin Naira miliyan uku.

Mataimakin Shugaban ’yan Sanda mai kula da Shiyya ta shida ta da ke Jihar Kuros Riba, Jonathan Towuru, ya sanar a Kalaba cewa ’yan sandan sun kwace kuɗin ne da bakin bindiga a hannun wani mai abin hawa.

A makon jiya ne aka zargi jami’an da ƙwayar kuɗin da bakin bindiga a hannun wani mutum da rundunar ta sakaya sunansa.

Yanzu haka waɗanda ake zargin an tuɓe masu kaki amma ana tsare da su ana bincike, da zarar an same su da laifi kotu za a turasu ta yanke masu hukuncin da ya dace.

KU KUMA KARANTA: ’Yan sanda za su tantance ’yan banga a Yobe

Mataimakin shugaban ’yan sandan ya ce waɗanda ake zargin su da karɓar cin hancin kuɗi Naira milyan uku daga wannun wani.

Ko a kwanan baya irin haka ta taba faruwa a kan babbar hanyar Kalaba zuwa Ikom inda aka kama wasu ’yan sanda kan karbar na goro.

Tafiya a kan hanyar na yawan zargin ’yan sanda da kula da shingen bincike a kan hanyar da yawan tatsar su kuɗi.

Continue Reading

'Yansanda

‘Yan sanda sun kama mutum 2 da ake zargin sace mahaifiyar Rarara

Published

on

Yan sanda sun kama mutum 2 da ake zargin sace mahaifiyar Rarara

‘Yan sanda sun kama mutum 2 da ake zargin sace mahaifiyar Rarara

Rundunar ’yan sandan Jihar Katsina ta sanar da cafke wasu mutum biyu bisa zargin hannu a garkuwa da mahaifiyar fitaccen mawaƙin siyasar nan, Dauda Kahutu Rarara.

Mai magana da yawun rundunar a Katsina, ASP Abubakar Sadiq Aliyu ya ce “muna tsare da mutum biyu kan lamarin, muna ci gaba da bincike.”

Tun farko, Kwamishinan tsaro na Jihar Katsina, Nasiru Mu’azu ya ce an sace dattijuwar ce a daren Juma’a a ƙauyen Kahutu da ke Karamar Hukumar Ɗanja.

Mu’azu ya ce waɗanda suka sace matar sun yi hakan ta hanyar bi ta bayan gida, inda suka sace ta ba tare da jami’an da ke tsaron gidan sun sani ba.

Ya kuma bayyana cewa tuni aka tura jami’an tsaro waɗanda suka bazama cikin dazuka domin bin sawun ’yan bindigar.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan bindiga sun yi garkuwa da mahaifiyar mawaƙi Rarara

Neptune Prime Hausa ta ruwaito shaidu a kauyen sun ce da misalin karfe daya na dare ne dandazon ’yan bindiga suka kutsa gidan dattijuwar suka yi awon gaba da ita.

“A kafa suka zo, ba su yi harbi ba a lokacin da suka ka yi awon gaba da ita cikin ’yan mintoci.

“Dattijuwar ba ta bijire musu ba a lokacin da suka memi ta biyo su.

“Duk da cewa ’yan bindigar sun samu wasu mutane a gidan, amma mahaifiyar Rarara kaɗai suka ɗauka.

“Babu wani yunƙuri da aka yi na tunkarar ’yan bindigar a lokacin da suke tafiya da ita saboda bindigogin da suke ɗauke da su,” in ji wani mazaunin ƙauyen na Kahutu.
Ya ce, “Watakila maharan sun bar baburansu ne daga nesa suka tako zuwa cikin ƙauyen a kafa.

“Muna rokon Allah Ya kuɓutar da ita cikin koshin lafiya domin tana taimaka mana sosai a wannan ƙauyen.

“Danta Rarara mai yawan taimakon al’umma ne, kuma ya kawo mana abubuwan ci gaba sosai a garinmu,” in ji shi.

Continue Reading

'Yansanda

‘Yan sanda sun kama kawali na ’yan bindiga

Published

on

'Yan sanda sun kama kawali na ’yan bindiga

‘Yan sanda sun kama kawali na ’yan bindiga

Daga Muhammad Kukuri 

Wani wanda yake kai wa ’yan bindiga karuwai domin yin lalata da su ya shiga hannun jami’an tsaro.

’Yan sanda sun bayyana cewa kawalin ya kuma ƙware wajen yin safarar makamai ga ƙungiyar jagoran ’yan bindiga mai suna Arɗo, wanda ake nema ruwa a jallo a yankin Kagarko da ke Jihar Kaduna.

An kuma gano cewa mutumin wanda yake harkar hada-hadar tura kuɗi ta PoS, shi ke kai wa iyalan ’yan bindiga kuɗaɗe a yankin na Kagarko.

Dubun kawalin ta cika ne a yayin wani samamen haɗin gwiwa da ’yan sanda suka gudanar a yankin.

Kwamishinan ’Yan Sandan Birnin Tarayya, ya sanar ranar Talata cewa wanda ake zargin ya shaida musu cewa shi ke tsara yadda ake kai wa ’yan bindiga karuwai da miyagun ƙwayoyi da ma’aikatan lafiya a duk lokacin da suke buƙata.

KU KUMA KARANTA: Ƴan sanda a Kano sun kai mutanen da ake zargi da sayar da dala ba bisa ƙa’ida ba kotu

“Ya kuma amsa cewa yana yin dakon kuɗi tare da rabawa ga iyalan ’yan bindiga.

“A cewarsa, kuɗaɗen da ya raba wa iyalan ’yan bindiga sun haura Naira miliyan ashirin,” in ji kwamishinan ’yan sandan.

Igwe ya ce wanda ake zargin ya tabbatar musu cewa ’yan bindigar da ke ƙarƙashin Ardo sun kai 15 kowannensu da bindiga ƙirar AK-47.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like