Jirgin ƙasa ya murƙushe wata mata da motarta yayin da take ƙoƙarin haye titin jirgin da ke unguwar Kubwa a Abuja ranar Alhamis.
![](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2022/12/FB_IMG_1671130839803.jpg)
Wani ganau mai suna Olisa Ogbechie, ya yi zargin cewa ‘yan sandan sun yi amfani da ƙarfi wajen fatattakar mutanen da ke son taimakawa daga wajen.
![](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2022/12/FB_IMG_1671130829156.jpg)
“A kokarin kubyutar da wanda abin ya rutsa da ita, da basu agajin farko da kuma ɗaukar yadda lamarin ya faru, ‘yan sandan da ke wurin suka hana ruwa gudu.
![](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2022/12/IMG-20221215-WA0081.jpg)
‘Yan sandan sun yi wa ni da wasu ‘yan tsiraru mummunan duka, yayin da suka yi ta harba barkonon tsohuwa a idona tare da wasu mutane biyu, sun nuna bindigogi yayin da suka tursasa mu barin wajen” inji shi.
Leave a Reply