Wani Mutum da ya saki matar shi ya nemi kotu ta bashi daman shafa nononta a duk ƙarshen mako

2
869

Wani magidanci mai suna Simon Williams ya nemi a ba shi damar cigaba da mallake nonuwan tsohuwar matarsa tare da morarsu ​​a wani ɓangare na sasantawar aurensa kamar yadda rahotannin intanet suka bayyana.

Da yake kwatanta nonon a matsayin ‘mai kima sosai’ a cikin takardar sakin aurensa, Simon ya ce, zai iya sadaukar da komai dan a bashi damar cigaba da mallakar nonon tare da morar sa.

Ya ce zai yiwa tsohuwar matar tasa kyautar mota don samun daman shafi nonon a duk karshen mako.

KU KUMA KARANTA:‘Yar Ganduje ta shiga cikin badaƙalar saki

“Waɗannan nonuwan da ke ƙirjinta suna tare da ni ta cikin wuya ko daɗi; a lokutan buƙata da kuma yin matashin kai a lokutan jin daɗi, ingancin rayuwata zai ragu sosai idan na rasa su.” In ji shi.

“A gaskiya abin ban tsoro ne, idan aka yi la’akari da ɗaya daga cikin dalilan da yasa na saki aurenta gaba xaya shine, don haka na ce ina son a bar min nono ta in cigaba da mora.”

Sai dai kuma tsohuwar matar tasa ta fusata ta ƙi amincewa da buƙatar, inda ta ce rashin ba ta damar mallakar ‘kayan sa na musamman a lokacin aurensu ya rage masa ƙima.

Lauyoyin da ke shari’ar sun ba da shawarar a rƙe nonon har sai an shawo kan lamarin.

2 COMMENTS

Leave a Reply