Connect with us

Labarai

Tinubu ya rattaba hannu kan dokar bai wa ɗalibai rancen kuɗin karatu

Published

on

Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya rattaba hannu a kan dokar bai wa ɗalibai bashin karatu.

Ya sa hannu kan dokar ce a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja a wannan Larabar.

Hakan na ƙunshe cikin wani saƙo da hadiminsa kan zaurukan sada zumunta, Dada Olusegun ya wallafa.

Dokar mai taken ƙudurin sauya wa dokar bai wa ɗalibai rancen karatu fasali ta 2024, an samar da ita ne domin kafa asusun tallafa wa ɗaliban makarantun gaba da sakandire.

A watan Nuwambar shekarar da ta wuce ne majalisar dokokin kasar ta amince da kudurin dokar, da ke neman kafa wata gidanauniyar da za ta riƙa ba ɗaliban manyan makarantun ƙasar bashin kuɗin makaranta.

KU KUMA KARANTA: Za mu ƙara albashin kowani ma’aikaci a Najeriya – Shugaba Tinubu

Sai dai ƙudirin ya fuskanci tasgaro dangane da wasu mas’aloli da suka shafi tsare-tsaren karɓa da biyan bashin kuɗin, lamarin da ya sanya Tinubu ya sake bitar ƙudirin tare da aike wa majalisa sabuwar buƙatar neman amincewarta.

A ranar 20 ga Maris, Majalisar Dattawa ta zartar da ƙudirin bayan nazarin rahoton kwamitinta da ke da alhakin kula da manyan makarantun da Asusun TETFUND da suka yi la’akari da kudirin.

Karkashin dokar bai wa ɗalibai rancen kuɗin karatu, za a ba da lamuni marar ruwa ga ’yan Najeriya da suka cancanci samun ilimi mai zurfi.

Masu ruwa da tsaki dai sun tabo batutuwan da suka shafi tsarin bayar da rancen kuɗin ga ɗalibai, musamman ma kan abin da ya shafi buƙatun cancanta, hanyoyin samar da kuɗaɗen, hanyoyin miƙa ɗalibai rancen da suka nema da kuma biyan bashin kuɗaɗen da sauran su.

Sabuwar dokar dai ita ce irinta ta farko a Najeriya a cewar Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Kasa, Femi Gbajabiamila.

Gbajabiamila wanda shi ne ya kawo kudurin dokar lokacin yana kakakin majalisa, ya ce dokar za ta inganta kasar domin babu wani yaron Najeriya da za a hana wa damar samun ilmi mai zurfi saboda rashin kuɗi.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like