Tag: Yan sanda
-
‘Yan sanda sun kwato bindigogi ƙirar AK-47 guda huɗu a Kano
Jami’an ‘yan sanda a jihar Kano sun kama bindigogi ƙirar AK-47 guda huɗu daga hannun wasu masu laifi a hanyar Kano zuwa Bauchi a ranar 25 ga watan Afrilu. Hakan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa mai ɗauke da sa hannun kakakin rundunar ‘yan sandan Kano SP Abdullahi Kiyawa a ranar Juma’a. Ya ce,…
-
PSC ta amince da korar jami’an ‘yan sanda 3, ta kuma rage ma’aikata 5 daga aiki
Hukumar da ke kula da aikin ‘yan sanda, PSC, ta amince da korar jami’an ‘yan sanda uku tare da rage masu muƙami biyar. Shugaban ‘yan jarida da hulɗa da jama’a na PSC Ikechukwu Ani ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya fitar ranar Laraba a Abuja, inda ya ce an tsawatar da wasu…
-
Hatsarin mota ya ci rayukan ‘yan sanda uku a Kaduna
Wasu ‘yan sanda uku sun rasa rayukansu a wani hatsarin mota da ya rutsa da su a garin Kidanda da ke karamar hukumar Giwa a jihar Kaduna. ‘Yan sandan na tafiya ne zuwa karamar hukumar Giwa bayan halartar bikin Hawan Dauche a birnin Zariya a ranar Lahadi, inda hatsarin ya afku da misalin karfe 9…
-
‘Yan sanda sun kama mutane 2 da ake zargi da binne dattijo da rai a Benuwe
Rundunar ‘yan sanda ta kama wasu mutane biyu da ake zargi da hannu a kisan wani dattijo a yankin Ikyve da ke ƙaramar hukumar Konshisha a jihar Benue. Dattijon mai suna Mista Ihwakaa ya rasu ne bayan da aka binne shi da ransa biyo bayan zargin da ake masa na maita da wasu matasa a…
-
Ya kashe direba don ya ajiye mota a inda aka hana – ‘Yan sanda
Rundunar ‘yan sanda a jihar Legas ta ce ta kama wani mutum mai shekaru 41, Tolulope Olowu da laifin daɓa wa wani Pablo mai shekaru 33 wuƙa, ya mutu har Lahira a kan ya ajiye mota a kan titinsu. Kakakin rundunar ‘yan sandan, Benjamin Hundeyin ya tabbatar wa kamfanin dillancin labarai na Najeriya afkuwar lamarin…
-
‘Yan sanda sun kama ‘yan fashi 44 a Kano
Daga Haruna Yusuf Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta kama wasu mutane 44 da ake zargin ‘yan fashi da makami ne da dillacin ƙwayoyi da ’yan daba a cikin kwanaki 10 na ƙarshen watan Ramadan a wani rangadi da suke yi a babban birnin jihar. Kakakin Rundunar ’Yan sandan Jihar Kano, SP Abdullahi Haruna Kiyawa…
-
‘Yan sanda sun ceto mutane 5, sun kama 17 da ake zargin masu garkuwa da mutane ne a Nasarawa
Rundunar ‘yan sanda a jihar Nasarawa ta kama wasu mutane 17 da ake zargi da yin garkuwa da mutane tare da ceto mutane biyar da suka mutu ba tare da an same su da rauni ba. Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, DSP Ramhan Nansel, ne ya bayyana hakan a lokacin da…
-
Rundunar ’yan sanda ta ba da miliyan 18 ga iyalan jami’anta da suka mutu
Kwamishinan ’yan sandan Jihar Gombe, Oqua Etim, ya miƙa wa iyalan jami’an rundunar su 25 da suka rasu a bakin aiki zunzurutun kuɗi har Naira miliyan 18 da dubu 500. Kwamishinan ya ce wannan kuɗi wani tallafi ne daga Babban Sifeton ‘Yan Sandan Najeriya, Alkali Baba Usman da kuma Hukumar Kula da Ayyukan ’Yan Sanda…
-
‘Yan sanda sun kama mutane 7 da suka kashe direban mota
Rundunar ‘yan sandan jihar Ondo ta ce an kama wasu mutane bakwai da ake zargi da jifan wani direba mai shekaru 35, ya mutu har Lahira a ranar 10 ga watan Afrilu. Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya yana cewa direban, Olorunfemi Tope, ya yi hatsari ya kashe mutum ɗaya tare da raunata wasu a hanyar…
-
Ta sayar da jaririnta ɗan wata 18 a kan kuɗi Naira 600,000 a Ogun – ‘Yan sanda
Rundunar ‘yan sandan jihar Ogun ta tabbatar da cafke wata mata ‘yar shekara 33, bisa zarginta da sayar da jaririnta mai watanni 18 a kan kuɗi Naira dubu 600,000 a yankin Sango-Ota da ke jihar. Hakan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa a Sango-Ota a ranar Litinin, ta bakin kakakin rundunar ‘yan sandan jihar,…