Tag: NEMA
-
Hukumar NEMA ta karɓi ‘yan Najeriya 146 da suka maƙale daga jamhuriyar Nijar
Hukumar bayar da agajin gaggawa ta ƙasa (NEMA) a ranar Larabar da ta gabata ta karɓi ‘yan Najeriya 146 da suka maƙale daga birnin Yamai na jamhuriyar Nijar. Dakta Nuraddeen Abdullahi, shugaban Hukumar NEMA reshen Jihar Kano ne ya bayyana haka a lokacin da yake karɓar waɗanda suka dawo a filin jirgin saman Malam Aminu…
-
Tinubu ya ba da umarnin mayar da NEMA, NAHCON ƙarƙashin ofishin mataimakin shugaban ƙasa
Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya amince da a mayar da Hukumar bada agajin gaggawa ta ƙasa, (NEMA), zuwa ofishin Mataimakin Shugaban Ƙasa domin kulawa, bisa bin dokokin kafa su daban-daban. Shugaban ya kuma amince da mayar da hukumar alhazai ta Najeriya NAHCON ofishin mataimakin shugaban ƙasa. Olusola Abiola, Daraktan yaɗa labarai na ofishin mataimakin shugaban…
-
Ba na neman zama shugaban ma’aikatan Tinubu – El-Rufai
Gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ya ƙaryata raɗe-raɗin da ake yaɗawa na cewa ya yi yunƙurin zama shugaban ma’aikata a zaɓaɓɓen shugaban ƙasa, Bola Tinubu. El-Rufai ya bayyana haka ne a Gombe ranar Asabar yayin da yake jawabi ga manema labarai. Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya (NAN) ya bayar da rahoton cewa El-Rufai ya je jihar…
-
Za a samu ambaliyar ruwa a jihar Kwara – NEMA
Hukumar bayar da agajin gaggawa ta ƙasa, (NEMA), ta sanar da mazauna jihar Kwara kan wata ambaliyar ruwa da ke tafe a bana 2023. Hukumar ta shawarci hakiman ƙauye da gundumomi da kuma malaman addini musamman na al’umma da su fara shirye-shirye domin daƙile illolin da ambaliyar ruwan za ta haifar. Hakan na ƙunshe ne…
-
Hukumar NEMA ta jaddada ƙudirinta na kwashe ‘yan Najeriya da suka maƙale a Sudan
Hukumar bayar da agajin gaggawa ta ƙasa (NEMA), ta jaddada ƙudirinta na kwashe ‘yan Najeriya da suka maƙale a ƙsar Sudan. Babban daraktan hukumar Mustapha Habib ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da kakakin hukumar Manzo Ezekiel ya fitar ranar Asabar a Abuja. Hukumar ta NEMA, ta ce tuni ta kafa wani kwamiti wanda…
-
Wasu jihohi a arewacin Najeriya za su fuskaci ƙarancin ruwan sama – NEMA
Jihohin Kaduna, Kano, Bauchi, Jigawa, Yobe da birnin tarayya Abuja za su iya fuskantar ƙarancin ruwan sama. Babban Darakta na Hukumar ba da agajin gaggawa ta ƙasa, NEMA, Mustapha Ahmed ne ya bayyana haka, cewa “babban birnin tarayya, Abuja, Kaduna, Bauchi, Kano, Jigawa da Yobe na iya samun ƙarancin ruwan sama a cikin wannan shekara”.…
-
Yan Najeriya fiye da 300 ne suka mutu sanadin ambaliya a bana
Daga Fatima GIMBA, Abuja Hukumomi a Najeriya sun ce mutane sama da 300 ne suka mutu, wasu fiye da 100,000 suka rabu da muhallansu sakamakon ambaliyar ruwa a fadin kasar tun daga watan Yuli. Ambaliyar ruwan ta kuma lalata gidaje da gonaki masu tarin yawa, a halin da ake ciki Najeriya tana fama da mummunar…
-
Gobarar tankar mai ta ƙona gini 10 a jihar Ogun–NEMA
Rahotanni daga jihar Ogun a Kudancin Najeriya na cewa wata tanka maƙare da lita 45,000 na man fetur ta kama da wuta tare da sanadin lalacewar gine-gine 10 a yankin Ifo. A cewar Hukumar ba da agajin gaggawa ta Najeriya, NEMA, lamarin ya faru ne da ƙarfe 7 na safiyar yau kan titin Olambe Matogun.…
-
An gano gawarwakin mutum 15 da suka nutse a Kogin Maiduguri
Daga Fatima GIMBA, Abuja Aƙalla gawarwakin mutum 15 aka gano a kogin Ngadabul a Maiduguri, babban birnin jihar Borno bayan afkuwar wata ambaliya. Kodinetan hukumar bayar da agajin gaggawa ta kasa NEMA a arewa maso gabas, Muhammad Usman, shi ya bayyana hakan a jiya Laraba, yayin tattaunawa da kamfanin dillancin labaran Najeriya a Maiduguri. Usman…
-
Gwamna Buni ya nemi ɗaukin Gwamnatin Taraiya kan ambaliyar Ruwan da ya Shafi Al’ummar Yobe
Gwamnan jihar Yobe Hon. Mai Mala Buni, ya buƙaci agajin Gwamnatin Tarayya daga Hukumar bada Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) domin tallafa wa yankunan al’ummomi daban-daban da ambaliyar ruwa ta shafa a yankunan ƙanana hukumomin Gulani, Gujba da sassan wasu ƙananan hukumomi a jihar. A halin da ake ciki, Gwamnan ya umarci Ma’aikatar Samarda Jin…