Connect with us

Kannywood

Sai ka ba ni jari na miliyan ɗari kafin In aureka -Safara’u kwana Casa’in

Published

on

Daga Saleh Inuwa, Kano

Korarriyar jarumar nan ta labari me dogon zango, Kwana Casa’in, safara’u, ta gindaya wasu sharruɗa ga duk wanda ke so ya aure ta, kana ta wallafa cewa “don Allah, masoyana ku taya ni tura wannan saƙon zuwa sauran groups don jama’a su ƙara gani ko zan samu mai cika waɗannan sharruɗan.

“Zan aureka idan ka cika dukkan waɗannan sharruɗan:

Na farko dole mu yi yarjejeniya a rubuce ka sa hannu ni ma in sa, cewar bayan ka aureni za ka barni in ci gaba da sana’ata wato rawa da waƙa.

Na biyu idan ba za ka barni ba to za ka bani jarin naira miliyan 100 domin in fara zuwa Dubai ina sayo kaya ina sayarwa.

Na uku dole ka bani kyautar gida a Kaduna da Abuja da kuma motar hawa wacce ta kai darajar naira miliyan 15.

Idan ka ga za ka iya to ka ajiye min number wayarka zan kira ka.”

Tun da aka kori jarumar daga shirin kwana Casa’in, saboda bidiyo da ta saki na baɗala, saita faɗa harkar rawa da waƙoƙi na habaici da zambo dan jan hankalin jama’a.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Kannywood

Kannywood ta ba wa Hisbah tabbacin goyon baya a Kano

Published

on

Bayan ce-ce-ku-ce, Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta sake zama da daraktoci da furdusoshi da jarumai da sauran masu ruwa da tsaki a Kannywood don tsaftace harkar fim da nufin kau da ayyukan baɗala a jihar.

A jawabansu daban-daban, Shugaban Ƙungiyar MOPPAN ta Ƙasa Dokta Ahmad Sarari da takwaransa na Jihar Kano Ado Ahmad Gidan Dabino da Shugaban Ƙungiyar Jarumai Alasan Kwalle sun nuna jin daɗinsu game da taron inda suka sha alwashin ba wa Hisbah goyon baya tare da alkawarin cewa nan gaba za a samu gyara a harkar fim ɗin.

Wannan shi ya kawo ƙarshen ce-ce ku-cen da aka yi ta yi game da ganawar Hukumar da ’yan fim na farko, wanda mafi yawansu suka ƙaurace wa bisa hujjar cewa Hisbar ba ta bi hanyar da ta dace wajen gayyatar su ba.

KU KUMA KARANTA: ’Yan Kannywood da dama sun ƙaurace wa taron da Hisbah ta gayyata a Kano

Hukumar ta sake miƙa musu goron gayyata a karo na biyu wanda suka amsa a ƙarƙashin jagorancin ɗan gidansu wato Shugaban Hukumar Tace Finafinai da Dab’i ta Jihar Kano Abba Almustapha.

Kwamanda-Janar na Hukumar Hisbah Shaikh Aminu Ibrahim Daurawa ya bayyana cewa ƙorafe-ƙorafe da suke yawan samu daga Kanawa da sauran sassan Najeriya kan yadda ’yan fim ke nuna abubuwan da suka saɓa wa addinin Musulunci da al’adun Hausawa a cikin finafinansu ya sa suka ga dacewar zama da masu ruwa da tsaki a harkar fim don laluɓo hanyoyin kawo gyara a cikin harkar.

“Ita Hukumar Hisbah an kafa ta ne don ta saita al’umma a kan koyarwar addinin tare da yi musu katanga daga aikata munanan ayyuka.

“Muna so a laluɓo hanyoyin da za a rage nuna abubuwa da suke na tir tare da ci gaba da nuna abubuwa da za su dabbaka addinin da kyawawan koyarwar al’adun Hausawa a harkar fim,” in ji Daurawa.

A nasa ɓangaren, Abba Almustapha ya bayyana cewa tuni ’yan fim din suka amince za su zama masu bin doka.

Abba Almustapha ya jaddada cewa nan ba da dadewa ba hukumomin biyu za su shirya taron ƙara wa juna sani da ’yayan Kannywood don ilimintar da su kan abin da ya shafi fim ta fuskar addinin Musulunci inda za a gayyato fitattun malaman Musulunci don tattauna tare da laluɓo hanyoyin da za a kai harkar fim ɗin ga tudun mun tsira.

Continue Reading

Kannywood

Ɗan wasan ƙwallon ƙafa Ahmed Musa, ya cika alƙawari, ya sayawa Karkuzu gida

Published

on

Kamar yadda Neptune Hausa ta kawo labarin cewa shahararren ɗan wasan Nijeriya Ahmed Musa MON ya yi alƙawarin sayawa Baba Karkuzu gida a yau Talata, alƙawari ya cika.
Alhamdulillah an sayi gida an kuma karɓi takardun gidan.

Kamar yadda kuke gani a hoto Baba Karkuzu ne riƙe da Jessy ɗin Ahmad Musa tare da takardan gidan shi cikin farin ciki da godiyar Allah (T).

Jarumin Kannywood, Karkuzu ya makance, yana kukan neman taimako

Ga waɗanda suka taimaka, Baba yace a isar masa da godiya a gare su, Ubangiji Allah ya sakawa kowa da alkhairi, Allah ya biyawa kowa buƙatar shi, wanda suka taimaka kuɗi da wanda suka taimaka da addu’a.

Dukkan mu Allah ya sakawa kowa da gidan Aljannah, Allah ya dube mu lokacin da muke cikin tsanani, Allah ya suturta mu da suturar shi mara yankewa, Allah ya rufa mana asirin mu. Ameen ya Allah.

Continue Reading

Kannywood

Jarumin Kannywood, Karkuzu ya makance, yana kukan neman taimako

Published

on

Fitaccen jarumin Kannywood, Abdullahi Shuaibu wanda aka fi sani da Karkuzu ya makance kuma yana fama da rashin lafiya.

Jarumin, wanda aka yaɗa bidiyonsa a shafukan sada zumunta, ya nemi taimakon kuɗi, inda ya bayyana cewa ya yi rashin lafiya tun watan Disambar 2020.

Shuaibu ya fara fitowa a masana’antar nishaɗantarwa ta Hausa a shekarun 1980 tare da shahararriyar wasan kwaikwayo mai suna Karkuzu na Bodara wanda ya sanya ake masa laƙabi da Karkuzu.

A zantawarsa da wannan jarida bayan faifan bidiyo, Karkuzu ya ce, “Yanzu na makance kamar yadda nake magana da ku. Ina matuƙar buƙatar taimakon kuɗi. Ba ni da abincin da zan ci da ciyar da iyalina.

KU KUMA KARANTA: Yadda mutuwar Alhaji Mala na shirin ‘Daɗin Kowa’ ta jijjiga Kannywood

“Gidan da nake zaune yanzu za a sayar. Idan sun sayar da wannan gidan, ban san inda zan dosa ba. Don haka ne nake neman taimako daga ‘yan Najeriya da su kawo min agaji.

A ƙalla ‘yan Najeriya su taimaka min sayan wannan gidan da nake zaune.”

Dangane da makanta, ya ce, “An min aiki sau biyu, amma a ƙarshe likitoci sun ce glaucoma ce, kuma ba zan sake gani ba. Na yarda da hakan a matsayin makoma ta. Amma ya kamata ‘yan Nijeriya su taimake ni. Kawo min gidan nan, da abinci.”

Masana’antar Kannywood na da ƙungiyoyi da dama, amma akwai zargin cewa ‘yan wasan kwaikwayo da dama ba sa kula da su idan ba su da lafiya kuma suna buƙatar taimako.

Zuwa haɗa wannan rahoto, ɗan wasan ƙwallon ƙafa na Najeriya Ahmad Musa ya ba shi kyautar naira dubu ɗari biyar, sannan ya ce a nemo gida na naira miliyan biyar zai saya masa.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like