Sadiya Haruna ta sake aure karo na 10

0
97
Sadiya Haruna ta sake aure karo na 10

Sadiya Haruna ta sake aure karo na 10

Jarumar TikTok, Sayyada Sadiya Haruna ta sake amarcewa a ranar Juma’a watanni kaɗan da mutuwar aurenta da jarumin TikTok Al Ameen G-Fresh.

A wani kati da ta wallafa a shafinta na Instagram, Sadiya ta bayyana sunan angon nata a matsayin Hon. Babagana Audu Grema.

An daura auren ne da misalin ƙarfe ɗaya bayan sallar Juma’a kamar yadda katin ya nuna a birnin Maiduguri da ke jihar Borno a arewa maso gabashin Najeriya.

KU KUMA KARANTA:Gwamnatin tarayya ta bai wa Rahama Sadau muƙami

Auren na zuwa mako guda bayan da jarumar ta TikTok ta bayyana a shirin tattaunawa na jarumar Kannywood Hadiza Gabon “Gabon Talk Show” inda Sadiya ta caccaki G-Fresh tare da bayyana matsalolin da suka kai ga mutuwar aurenta da shi.

Auren har ila yau na zuwa ne kwana guda bayan da shirin na Gabon ya watsa tattaunawar mayar da martani da G-Fresh inda shi ma ya yi ta sukar tsohuwar matar tasa – mafi aksarin lokuta a kaikaice.

Leave a Reply