Connect with us

Labarai

Rundunar sojin sama taci galaba kan Halilu Tubali, ƙasurgumin dan fashin daji a Zamfara

Published

on

Hukumomi a Najeriya sun ce sun tarwatsa sansanin wani ƙasurgumin ɗan fashin daji da ya addabi sassan jihohin Zamfara da Katsina, tare da gomman yaransa.

Rundunar sojin saman ƙasar ta tabbatar wa BBC cewa an kashe Halilu Tubali da yaransa a wani hari da jirgin yaƙi da dakarunta suka kai a ƙarshen makon jiya.

Majiyoyi sun ce yana ɗaya daga cikin shugabannin ‘yan fashin daji da suka fi kuɗi, kuma ya ƙware wajen fasa-ƙwaurin makamai.

Hukumomin sun ce sun samu labarin cewa wannan kasurgumin ɗan fashin daji yana gudanar da wani taro ne tare da yaransa masu yawa, ko da yake dama sun dade suna fakonsa, da wuraren da yake mu’amalarsa.

A cewar hukumomin Halilu Tubali babban mai shigo da makamai ne ga ‘yan fashin daji da ke yankin Zamfara da Katsina, baya ga na shi aikin da yake yi a yankin Sububu da bayan Ruwa a karamar hukumar Anka a jihar ta Zamfara.

Ka zalika an tarwatsa wani rumbun ajiyar makaman Tubali a wannan hari, kamar yadda daraktan hulda da jama’a na rundunar sojin sama air kwamado Edward Gabkwet, ya bayyana mani.

Sai dai bayanan da na tattaro daga yankin na Muradun sun nuna cewa akai-akai ‘yan bindigar ke yin taruka domin tsara yadda za su rika kai hari kan al’umma ko kuma jami’na tsaro.

Duk da dai babu wani cikakken adadin mutanen da aka kasha ko aka jikkata, amma ta tabbata an lalata sansanin Halilu Tubali wanda hakan a cewar rundunar sojin saman ka iya samar da kwanciyar hankali a yankin na Zamfara da Katsina ganin mummunan tasirin da yake da shi ya yankin.

1 Comment

1 Comment

  1. Pingback: Rundunar sojin sama taci galaba kan Halilu Tubali, ƙasurgumin dan fashin daji a Zamfara – LEGEND FM DAURA

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like