Connect with us

Boko Haram

Rashin tsugunar da ‘yan Boko Haram da suka miƙa wuya babban haɗari ne- Barista Bulama Bukarti

Published

on

Daga Fatima GIMBA, Abuja

Masana harkokin tsaro a Najeriya sun ce akwai babban haɗari idan har ‘yan kungiyar Boko Haram din da suka miƙa wuya suka rasa matsugunni.

Masanan sun yi tsokacin ne bayan da hukumomi a Jihar Borno da ke arewa maso gabashin ƙasar, suka ce ana fama da ƙarancin wurin ajiye dubban ‘yan ƙungiyar ta Boko Haram da suka miƙa wuya.

Barista Audu Bulama Bukarti, mai sharhi ne kan lamurran tsaro, ya shaida wa BBC cewa akwai hatsarin gaske idan har gwamnati ko hukumomin tsaro suka gaza wajen samar da matsugunnai ga wadannan ‘yan Boko Haram din.

“Babban hatsarin shi ne za su iya kuɓucewa su koma in da suka fito wato ƙungiyarsu, saboda da yawa daga cikinsu yunwa ko rashin yarda da wani abu a kungiyar ne ya sa suke fita daga kungiyar su mika wuya.”

Masanin tsaron ya ce idan har suka je sansanin suka ga babu abincin da za a ci a koshi sannan rayuwa ta ki dadi a wajen, ko kuma duk da sun mika wuya an ki yi musu abin da ya dace misali na rashin mayar da su cikin al’umma, to babban abin da za su fara yi shi ne su gudu su koma kungiyarsu.

Barista Bukarti, ya ce “Abu na biyu za su iya wanke kan wasu waɗanda su ba ‘yan kungiyar ta Boko Haram ba ne sun kuma hadu da su a irin zaman sansani, sai su wanke su don su koma ƙungiyar tasu.”

Ya ce abu na uku tun da ita ƙungiyar Boko Haram din na jin haushin waɗanda suka miƙa wuyan, to za ta iya kitsa hari ta kai irin wuraren da aka ajiye su don ta kashe su.

Masanin tsaron ya ce dole idan gwamnati na son ƙare duk abubuwan da ya lissafa, to na farko shi ne gwamnati ta fito ta faɗa wa mutane gaskiya a kan matsayin mutanen da suka miƙa wuyan.

Ya ce,” Abu na biyu shi ne gwamnati ta yi tsari mai kyau tun da dai za a ci gaba da samun irin waɗannan mutanen da za su rinƙa miƙa wuya.”

Barista Bukarti, ya ce dole sai gwamnati ta smaar da isassun sansanoni na ajiye irin waɗannan mutane da kuma isassun kayan kula da su ciki har da tsare su daga hare-hare, da tabbatar da cewa ba su koma kungiyar ba.

Ƙarin bayani

Kwamandan rundunar yaƙi da matsalar tsaro a yankin Arewa maso gabashin Najeriya, wadda ake kira ”Operation Haɗin Kai”, Manjo Janar Chris Musa, ya ce ya zuwa yanzu tsofaffin ‘yan ƙungiyar kusan dubu sittin da bakwai (67,000) ne suke jiran a karbe su, sai dai wurin da ake da shi ba zai dauke su ba.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Boko Haram

An tabbatar da mutuwar masu juna biyu a cikin harin da aka kai a Borno

Published

on

An tabbatar da mutuwar masu juna biyu a cikin harin da aka kai a Borno

An tabbatar da mutuwar masu juna biyu a cikin harin da aka kai a Borno

An kasha aƙalla mutane 18, yayin da wasu 30 suka jikkata bayan wasu jerin hare-haren da ake zargin wasu mata ‘yan ƙunar baƙin wake ne suka kai a jihar Borno a jiya Asabar, in ji shugaban hukumar bayar da agajin gaggawa ta yankin.

Borno dai na cikin shekaru 15 na hare-haren masu iƙirarin kishin Islama wanda ya yi sanadiyar mutuwar dubban mutane tare da raba wasu miliyoyi da humallan su.

Duk da cewa sojojin Najeriya sun rage ƙarfin mayaƙan, amma har yanzu suna kai munanan hare-hare kan fararen hula da kuma wuraren tsaro.

KU KUMA KARANTA:Gobara ta tashi a matatar man Ɗangote

Barkindo Saidu, shine babban Daraktan Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Borno, ya ce wasu da ake zargin ‘yan ƙunar baƙin wake ne suka kai hari daban-daban a wajen bikin aure da jana’iza da kuma asibiti, inda suka kashe mutane tare da jikkata wasu da dama a garin Gwoza.

Saidu ya ce an tabbatar da mutuwar mutum 18, adadin da ya haɗa da ƙananan yara da manya da ma mata masu juna biyu.

Sai dai babu wata ƙungiyar ko wani mutun da ya ɗauki alhakin kai wannan harin.

Boko Haram da ISWAP da ta ɓalle kanta, su ne ƙungiyoyin ‘yan bindiga da suka fi yawan gudanar da ayyukan su a jihar Borno, wani babban yanki na karkara mai girman gaske.

Continue Reading

Boko Haram

Boko Haram sun kashe manoma 15 a jihar Borno

Published

on

Wasu da ake zargin ‘yan ƙungiyar Boko Haram ne sun kashe aƙalla mutane 15 a hare-haren da suka kai kan wasu ƙauyuka biyu a ƙaramar hukumar Jere ta jihar Borno.

Kamar yadda rahoton Daily Trust ta ruwaito, ‘yan ta’addan sun kai farmaki ƙauyen Ƙofa ne da tsakar dare inda suka fara harbe-harbe ba da daɗewa ba, wanda har zuwa safiyar Juma’a.

An tattaro cewa maharan sun kuma kai hari a ƙauyukan Molai Kura da Molai Gana inda suka yi ta yanka mutane da ba a tantance adadinsu ba.

KU KUMA KARANTA: Yadda ‘yan Boko Haram suka yiwa masunta 29 kisan gilla, suka jikkata 9 a Gamborun Ngala

Lamarin dai ya sa mazauna yankin da dama sun ƙauracewa gidajensu zuwa wani daji da ke kusa.

Wani jigo a ƙungiyar ’yan banga, Bukar Ali-Musty, ya shaida wa jaridar cewa manoman na aikin gonakinsu ne a kusa da Molai, da ke wajen birnin Maiduguri, a ranar Alhamis ɗin da ta gabata, inda ‘yan tada ƙayar bayan suka kai musu hari suka sare kawunansu.

“Aƙalla gawarwaki 15 ne aka kwashe a safiyar yau, an kai hare-haren ne jiya (Alhamis).

“An sare kan manoma bakwai a lokacin da suke aikin gonakinsu, sannan maharan sun kuma yanka wuya ga wasu fararen hula takwas da ba su da illa a gidajensu,” in ji shi.

Wani memba a ƙungiyar ‘civilian JTF’ da ke cikin tawagar da aka kwashe, ya nuna damuwarsa kan hare-haren, yana mai cewa dole ne duk masu ruwa da tsaki su farka don ganin ba a ci gaba da faruwa ba.

“Abin takaici ne ci gaba idan aka yi la’akari da ci gaban da muka samu a cikin watanni ba tare da an kai wa al’umma hari ba.

“Ina can da safe. Ba zan iya tunanin ganin an yanka ’yan uwana kamar rago ba.

Dukkanin gawarwakin da muka ƙwato an same su ne a cikin kwance cikin jini, kuma ina ganin dukkanmu muna buƙatar mu tashi tsaye domin tunkarar wannan maƙiyin zaman lafiya,” inji majiyar.

Continue Reading

Boko Haram

ISWAP ta kashe mutane uku da jikkata sojoji takwas a Borno

Published

on

Aƙalla ‘yan gudun hijira guda uku ne aka kashe tare kuma da jikkata wasu 13 ciki har da sojoji guda takwas a wasu mabambantan hare-hare da ƙungiyar ISWAP ta kai ƙaramar hukumar Damboa na jihar Borno.

An ruwaito cewa lamarin ya faru ne lokacin da ‘yan gudun hijira guda huɗu da ke zama a sansanin Lowcost a Damboa suka fita domin neman itacen hura wuta lokacin da mayaƙan suka buɗe musu wuta, inda suka kashe uku nan take yayin da sauran mutane kuma suka tsere da raunuka.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa tun da farko ISWAP ɗin sun jikkata wasu sojoji da kuma fararen hula yayin wani hari da suka kai yankin Talala a ranar Talata duk a Damboa.

Wata majiyar tsaro ta tabbatar da cewa sojoji sun kashe mayaƙan na ISWAP da dama a wani hari da suka kai musu.
Majiyar ta ce wani jrgin sama na sojoji ya je Damboa a jiya Alhamis, inda ta ɗebo sojoji da suka jikkata zuwa Maiduguri domin yi musu magani.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like