Connect with us

Jan hankali

NUJ jihar Yobe, ta nuna rashin jin daɗi da ƙara farashi da masu gidajen mai suka yi

Published

on

Daga Ibraheem EL-TAFSEER

Ƙungiyar ‘yan jarida ta Najeriya (NUJ) reshen jihar Yobe ta bayyana rashin jin daɗin ta game da halin rashin kishin ƙasa da wasu masu gidajen man fetur da ma’aikata suka yi a Damaturu, babban birnin jihar Yobe da sauran ƙananan hukumomin jihar, dangane da ƙarancin man fetur da aka samu a yau da kuma ƙaruwar farashin mai ɗin, wanda hakan ya jawo dogon layi a gidajen man.

A wata takarda da ƙungiyar ta fitar, wanda shugaban ƙungiyar ‘yan jarida na jihar Yobe, Kwamared Rajab Mohammed da sakatatensa Alhassan Sule Mamudo suka sa wa hanu, ta bayyana cewa, ƙungiyar ta damu matuƙa da halin da ‘yan jihar ke ciki masu son zaman lafiya.

KU KUMA KARANTA: Cire tallafin man fetur ya jawo hauhawar farashin mai a Najeriya

Don haka muna ƙira ga hukumomin tsaro, hukumomin gwamnati, hukumomin da abin ya shafa da duk masu ruwa da tsaki da su gaggauta ɗaukar matakan da suka dace don ganin an kawo karshen wannan mummunan yanayi da ke iya lalata tattalin arziƙin al’umma.

Za mu iya kwatanta shi a matsayin zagon ƙasa ga tsarin dimokuraɗiyyar Najeriya. Ƙungiyar za ta ci gaba da sanya ido kan lamarin tare da sanar da ‘yan ƙasar kan duk wani ci gaba mai kyau tare da yin ƙira ga kowa da kowa da su kwantar da hankula domin za a shawo kan lamarin cikin ruwan sanyi.

1 Comment

1 Comment

  1. Pingback: Ƙananan Hukumomi uku na Yobe suna kashe miliyan 299.1 a ayyuka | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

CBN

Jabun kuɗaɗe sun bazu a gari — CBN

Published

on

Babban Bankin Najeriya (CBN) ya ja hankalin ’yan Najeriya kan jabun takardun kuɗin ƙasar da ke yawo a cikin al’umma a sakamakon raɗe-raɗin da ake yaɗawa na ƙarancin tsabar kuɗi.

Kakakin CBN, Hakama Sidi Ali ta shawarci al’umma da su kasance masu lura ganin cewa masu jabun kuɗaɗe na amfani da su a matsayin kuɗin mota ko a wurin yin cefane da gidajen abinci sauransu.

Sanarwar ta CBN ta ce “Dokar CBN ta tanadi hukucin ɗaurin aƙalla shekaru biyar ga duk wanda ya buga jabun kuɗaɗe.

“CBN na aiki da hukumomin tsaro da na hada-hadar kuɗaɗe wajen ganowa da ƙwace jabun kuɗaɗe da kuma tsare masu buga su.” in ji jami’ar.

Daga nan sai ta umarci bankuna, ’yan canji da sauran cibiyoyin hada-hadar kuɗaɗe da su ɗauki matakan da suka dace wajen ganowa da kuma hana yaɗuwar jabun kuɗaɗe.

Ta ƙara da cewa, “ana ƙira ga jama’a su kai ƙarar duk wanda suka ga yana yin jabun kuɗaɗe ga ofishin yan sanda ko na CBN mafi kusa.

Continue Reading

EFCC

EFCC ta fitar da matakai takwas na kare kai daga masu damfara da katin ATM

Published

on

Hukumar da ke yaƙi da masu yi wa tattalin arzikin ƙasa zangon ƙasa a Nijeriya, EFCC ta koka kan yadda take yawan samun rahotanni na waɗanda aka cire wa kuɗi daga banki ba tare da saninsu ba kuma akasari ta ATM.

Hukumar ta ce akasarin ƴan damfarar sun fi samun bayanan jama’a ko katin ATM ɗin mutane a wuraren cirar kuɗi na ATM ko kuma masu POS.

EFCC ta yi gargaɗi kan cewa ƴan damfarar suna amfani da katin ATM na bankin mutumin da suke so su yaudara, bayan haka sukan je wurinsa da niyyar taimako idan ya shiga ruɗani a gaban ATM.

Hukumar ta ce ƴan damfarar kan yi sauri su yi wa kwastoman bankin musaya da katinsa bayan su haddace lambobin sirrinsa a lokacin da suke ƙoƙarin taimakonsa, wanda daga baya sai su cire kuɗin da ke asusun ajiyarsa.

Dangane da haka ne hukumar ta fitar da hanyoyi takwas waɗanda take ganin idan jama’a sun bi su za su samu kariya daga masu damfarar:

KU KUMA KARANTA: EFCC za ta gurfanar da sojojin saman Najeriya a kotu kan zargin damfara a intanet

  1. Akwai buƙatar ajiye kati a aminctaccen wuri. Duk lokacin da ka karɓi katinka bayan cire kuɗi, ka tabbata katinka ka karɓa ba wai wanda ke kama da katinka ba.
  2. A rinƙa duba sauran kuɗin da ke asusu (balance) domin dubawa ko an cire kuɗi daga asusu.
  3. Saka ƙararrawa domin lura da duk wani abu da ya shafi asusun ajiya ko katin banki.
  4. Rufe lambobin da ake latsawa a jikin ATM ko POS da hannu a lokacin da ake saka lamobin sirri domin cire kuɗi ko wani amfani.
  5. A rinƙa neman taimako daga jami’an banki, ka da ka yi saurin biyan kuɗi ko cire kuɗi.
  6. A ƙira banki domin toshe katin ATM a duk lokacin da aka lura kati ya maƙale a cikin ATM ko kuma duk lokacin da aka lura da wani lamari wanda yake ba daidai ba.
  7. A tabbata an san lambar da za a iya toshe ATM da ita tare da amfani da ita cikin gaggawa a duk lokacin da aka ɓatar da katin ko aka sace shi.
  8. A latsa lambobin USSD na 966911# da kuma bin matakan da suka biyo baya domin toshe katin ATM nan take.
Continue Reading

'Yansanda

Yadda ɗan damfara ya yaudari ’yan sandan Ngelzarma, da wasu mutane biyu: Labarin Bello Muhammad ​​da Sulaiman Garba

Published

on

Bello Muhammad mazaunin garin Ngelzarma ne, a ƙaramar hukumar Fune ta jihar Yobe, Najeriya. Yana gudanar da sana’ar cajin waya, inda mutane ke kawo wayoyinsu ayi musu caji, kuma su biya shi kuɗin aikin sa.

Wani ɗan damfara ya zo shagonsa, sai ya ga wata waya mai tsada, sai ya yanke shawarar cewa sai ya mallaki wannan wayar, har da wasu wayoyinma. Kai tsaye ya nufi ofishin ‘yan sanda, da rigar ciki ta ‘yan sandan Najeriya, da katin shaida na ƙarya.

Ya gabatar da kansa a matsayin CID a hedkwatar, kuma ya ba da rahoton cewa ya bi diddigin wata wayar da aka sace (Tracking) zuwa wani wurin cajin waya, inda a take suka ba shi umarnin ya je ya kawo wayar, da kuma mai kula da shagon wayar. Don haka ya je shagon Muhammad Bello ya gaya masa irin labarin da ya faɗawa ‘yan sanda cewa ya bi diddigin wata waya da aka sata zuwa shagonsa, zai kai Muhammad ​​da wayar ofishin ‘yan sanda.

Muhammad da sanin cewa bai aikata komai ba, ya bishi har ofishin ‘yan sanda da ke bayan gari. ‘Yan sanda ba su ji ta bakin Muhammad ​​ba, suka cire masa kaya da ‘yan mukullinsa da wasu kayansa sannan suka kulle shi.

Muhammad Bello, mai shagon charjin waya

CID na bogi ya ɗauki wayar, da nufin fita daga ofishin ‘yan sandan, inda ya ba su lambar waya ta bogi tare da katin shaidar ƙarya. Da aka tambaye shi ko yana da wata shaida ta bin diddigin, (Tracking certificate), sai ya ce yana tare da sajan nasa a cikin gari, kuma zai je ya kawo.

Ya ɗauki babur ya wuce kai tsaye shagon Muhammad, ya umarci mai tsare shagon wayar daya kawo wayar maigidansa, suna kan binciken maigidan nasa ne a ofishin ‘yan sanda, aka aiko shi ya karɓi wayoyin.

Mai shagon ya gane mutumin a matsayin wanda suka fita tare da ubangidansa, ya fito da wayoyin Muhammad ​​guda biyu ya miƙa wa CID na bogi. Shi ko ɓarawo yaga ya mallaki wayoyin sata guda uku a hannunsa, sai ya arce.

A ofishin ’yan sanda kuwa, har kusan ƙarfe 3 na rana babu labarin CID da ya ce zai je ya dawo. Muhammad ya gaji, sai ya fara yin tambayoyi kamar haka ”ta yaya za a kama ni laifin da ban yi ba”,?
Abin da ban san komai game da shi ba?’

”Aikina shi ne cajin waya, babu ruwana da matsalar mallakin waya. Ina ganin ya kamata a yi cikakken bincike”.

Sulaiman Garba, wanda aka sace ma waya

”Mutumin da ya kawo wayar shagona ya kamata a yi ma tambayoyi, ba ni ba”. Inji Muhammad

‘Yan sandan sun amsa da cewa suna jiran CID ya dawo ne har yanzu. Muhammad ya ba da shawarar su ƙira shi ta waya, suka yi ta ƙira amma ba su samunsa, lambar bogi ce. Haka dai aka ci gaba da jira har ƙarfe biyar na yamma, a lokacin ne dangin Muhammad suka yanke shawarar ziyartar ‘yan sanda domin jin ba’asi.

Sun koka da yadda mutane ke jiran Muhammad a shagon domin karɓar wayoyinsu, don haka akwai buƙatar ‘yan sanda su sake shi. Sannan kuma sun yi tambaya game da inda CID yake, amma ‘yan sanda sun kasa yi musu cikakken bayani.

’Yan’uwan Muhammad ​​sun nuna rashin jin daɗinsu da jami’an da kawai suka yarda da wani labari daga wani baƙo ba tare da wata hujja ko shaida ba saboda ya zo da mari a hannun sa, da katin shaidar ƙarya.

Daga nan ne hankali ya fara tashi. ASP Musa Nuhu ya umarci Sajan da jami’an sa, da su je su nemo wannan CID ɗin a duk inda yake. Bayan sun shafe sa’o’i suna bincike, sai suka sanar da ɓacewarsa. ASP ya shaidawa Muhammad ​​cewa ”tare muka ganku, don haka babu abin da za mu iya yi”.

Ngelzarma chaji Ofis

Aka sallami muhammad, ya kai maganar wajen Lawani, inda Lawanin ya yi alƙawarin taimaka wa Muhammad. Sai dai abin takaicin shi ne, Lawanin bakinsu ɗaya da jami’an tsaro, don haka ya ƙira su, suka tabbatar da faruwar lamarin. Yayin da ya ke ƙiran ‘yan sanda, wasu ma’aurata da ke wurin kan batun aure sun ji shi a lokacin da ya ƙira ‘yan sanda.

Muhammad ​​ya ji ba a neme shi ba har an kwana, sai ya koma. Lawanin ya ce har yanzu bai gana da jami’an ba, don haka ya ƙara haƙuri. Muhammad ya koka da cewa mai wayar, mai suna Sulaiman Garba ya matsa masa sai ya biya shi wayarsa. “Na yi masa bayani cewa wayar tana wurin ‘yan sanda, amma yaƙi yarda da bayanina.”

Lawanin ya yi alƙawarin sasanta lamarin washegari. A washegarin, Lawanin Ya gana da ’yan sanda a cikin wani taron sirri, yayin da Muhammad ​​ke zaune a gindin wata bishiya a waje. Bayan sun tattauna ne suka yanke shawarar cewa Muhammad ​​ya kawo kuɗi su yi amfani da su wajen gano wayoyi ukun da aka sace.

Yanzu dai Muhammad yana cikin wani hali, ga ɓatan wayoyinsa, ga ɓatan wayar kwastomansa, a dalilin sakacin ’yan sanda.

Jaridar Neptune Prime ta ƙira PPRO na Damaturu, Dungus AbdulKareem don jin ta bakinsa, sai yace bai san komai ba game da lamarin. Bayan mun masa bayani, ya nuna rashin jin daɗin faruwar hakan, kuma ya umarce mu da mu bawa su Muhammad lambarsa nan take, domin ya taimaka musu.

Har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, ba mu san yadda ta ƙare ba tsakanin waɗanda abin ya shafa, PPRO, da kuma sashin ‘yan sanda na Ngelzarma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like