Connect with us

Labarai

Nasara ta zata bai wa ibo damar shugabancin Najeriya – Atiku

Published

on

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, ya yi alƙawarin sanya tashar jiragen ruwan Onitsha ta yi aiki idan aka zaɓe shi a matsayin shugaban ƙasa a zaɓen 2023.

Atiku Abubakar, tsohon mataimakin shugaban, ya yi alƙawarin ne a ranar alhamis a taron yaƙin neman zaɓen jam’iyyar PDP da aka gudanar a Awka jihar Anambra.

Ya ce: “Da isowarmu a yau mun ziyarci Gwamna Soludo kuma ya ce min ya yi imani cewa zan yi aiki idan na yi nasara.

“Don haka, ya buƙace ni da in sake gina dukkan hanyoyin tarayya da kuma shawo kan matsalar zaizayar kasa a jihar, saboda ana daukar Anambra a matsayin hedikwatar zaizayar ƙasa a ƙasar nan.

Kuma na yi masa alƙawari zan yi hakan.

“Na kuma yi alƙawarin yaye kogin Neja kuma in tabbatar da cewa tashar jiragen ruwa ta Onitsha ta fara aiki, idan kun zaɓi PDP a zaɓe mai zuwa.

KU KUMA KARANTA:Dala Biliyan 10 zan ware don inganta rayuwar matasa tare- Atiku Abubakar

“Za mu kuma inganta jihar don samar da ayyukan yi ga matasan mu,” in ji shi.

Atiku ya ce shi ne zai zama matakin tabbatar da shugabancin Igbo idan aka zabe shi a shekarar 2023.

“Zan zama matattakalar shugabancin Igbo. Na nuna hakan ta hanyar ayyukana ne domin wannan shi ne karo na uku da zan yi takara da ɗan kabilar Ibo a matsayin abokin takarata.

“Idan kuna son samar da shugaban kasa, to ku zaɓi Atiku/Okowa.

“Na gode muku da wannan kyakkyawar tarba, kuma mun yi alkawarin ba za mu ba ku kunya ba,” in ji Atiku.

Shima da yake jawabi, Gwamna Ifeanyi Okowa, mataimakin ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP, ya yaba wa shugabannin jam’iyyar bisa gagarumin yaƙin neman zaɓe na al’ummar jihar Anambra.

Ya ce “Muna ƙira gare ku da ku zaɓi PDP a babban zaɓe.
“Ɗan takararmu na shugaban kasa, Atiku, shi ne ya fi kowa gogewa a cikin dukkan ‘yan takarar da ke takara, kuma ya ƙuduri aniyar sauya fasalin Najeriya,” in ji Okowa.

A nasa jawabin, Iyorchia Ayu, shugaban jam’iyyar PDP na ƙasa, ya bukaci jama’a da su kaɗa ƙuri’a ga jam’iyyar PDP, inda ya bayyana jihar Anambra a matsayin jihar PDP ba ta APGA ba.

“PDP ta fara ne a Anambra tare da shugabanmu, Dr Alex Ekwuene, don haka Anambra ta PDP ce ba APGA ba.
APGA ɗan PDP ne kuma nan gaba za mu dawo da APGA gidansu wato PDP.

“ ‘Yan ƙabilar Igbo, musamman a Anambra, masu ruwa da tsaki ne a Najeriya, domin babu wani ƙauye da za ku je a ƙasar nan da ba za ku ga ɗan ƙabilar Igbo ba. Wannan ya sa sun fi zama ‘yan ƙasa.

“Ina rokon ku da ku zaɓi PDP saboda muna da ƙwararre mai cancanta, wanda ɗan kasuwa ne kamar ku, kuma surikinku. Wani lokaci surikinku ya fi ɗanku.

“Don haka, ku je ku karɓi katunan zaɓe na dindindin ku zaɓi Atiku/Okowa. Wannan tawagar za ta magance matsalolin tsaro na Najeriya, da daidaitawa da kuma sauya yanayin kasar nan,” in ji shi.

A nasa jawabin, Farfesa Obiora Okonkwo, darakta janar na yaƙin neman zaɓen Atiku/Okowa, ya bukaci jama’a su zaɓi Atiku a matsayin shugaban ƙasa a zaɓen 2023.

Okonkwo ya ce nasarar da ya samu a rumfunan zaɓe, za ta ba igbo damar shugaban cin kasar .

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like