Connect with us

Labarai

Na shiryar tsaf don daidaita sahun mambobin ƙungiyar masu maganin gargajiya a jihar Yobe – Alhaji Ado

Published

on

Daga Sani Gazas Chinade, Damaturu

A ƙoƙarin dawo da martabar ƙungiyar masu maganin gargajiya (NANTMP) a jihar Yobe sabon shugaban riƙo na ƙungiyar, Alhaji Ado Yaro mai maganin Gargajiya kuratandu Gashuwa ya bayyana cewar a halin da ake ciki ya shiryar tsaf don daidaita sahun ƙungiyar, sakamakon tafiyar da a baya ta ke yi ba bisa bin hanyoyin da suka dace ba.

Alhaji Ado ya bayyana hakan ne a tattaunawar sa da wakilinmu a garin Damaturu dangane da yadda ya ke ga matsalar ƙungiyar jim kaɗan da karɓar iagoranci daga tsoffin shugabannin ta kafin gudanar da zaɓe nan gaba. Ya ƙara da cewar, a matsayin sa na shugaban riƙo na wannan ƙungiyar a jihar Yobe ya ɗaura ɗamarar ganin an inganta wannan ƙungiyar ta masu maganin gargajiya a jihar ta yadda shi da sauran shugabannin riƙo za su yi duk abin da za su iya yi don ganin sun daidaita sahun mambobin da kuma ita kanta ƙungiyar don komawa cikin hayyacin ta daga doguwar sumar da ta yi a baya.

“Alhaji Ado ya ƙara da cewar, duk da cewar ba’a daɗe da rushe tsoffin shugabannin wannan ƙungiyar ba, amma duk da haka a ganin sa an san zai iya ne ya sanya mambobin ƙungiyar da masu ruwa da tsakiya na ƙungiyar suka ɗauko ni don ɗora min alhakin riƙe wannan ƙungiyar har kaiwa ga lokacin da za’a sake zaɓo sabbin shugabannin da za su shugabancin ƙungiyar kamar yadda tsarin Mulkin ta ya ke.”

Da wakilinmu ke tambayar sa akan ko wane hoɓɓasa zai yi don ganin ya ɗora wannan ƙungiyar ta su kan tafarkin da ya dace? “A nan sai ya kaɗa baki ya ce,  a halin da ake ciki shi da sauran sabbin shugabannin ƙungiyar suna hoɓɓasa don ganin sun za ga dukkannin ƙananan hukumomin jihar 17 don ganawa da mambobin wannan ƙungiyar da nufin ganawa da su don wayar musu da kai yadda za su tsarkake wannan sana’a ta sayar da maganin gargajiya tare da faɗakar da su ta yadda za su riƙa sarrafa magungunan ba tare da kaucewa hanyar ba ko kuma gurɓata shi ba lura da cewar al’umma ne ke amfani da shi don samun waraka.”

KU KUMA KARANTA: Ko kasan maganin ciwon haƙori sadidan?

Shugaban ya kuma ƙara da cewar babban abin da ya ƙara mana ƙarfin gwiwar wannan ziyarce-ziyarce da suka shirya yi ga ƙananan hukumomin jihar shi ne don ƙoƙarin tantance yawan mambobin da muke da shi kamar yadda hukumar lafiya ta jihar Yobe ta bamu shawarar yi don sanin yadda za mu yi rijistar kowane mamban wannan ƙungiyar don tafiya daidai da zamanin, lura kuma da cewar hukumar lafiya ta jihar na da shirin samar da ƙudirin buɗe ɓangaren masu maganin Gargajiya a wasu asibitoci uku da ke jihar wadda kan hakan ne ma muka bazama don tantance adadin mambobin mu.

“Haka nan za kuma mu bi hanyoyi don sake daidaita sahun masu maganin gargajiya a jihar ta Yobe yadda za mu sa dokar daina tallar magani ta yadda wasu ke ƙure sautin amsa kuwa ta yadda ake riƙa damun mutane da ƙarar amsa kuwa (Loudspeaker) fiye da ƙima da kuma yawaitar furta maganganun batsa yayin tallar maganin a tituna da kasuwanni da kuma wuraren taruwar jama’a da makamantan haka. “

“Don haka mun ƙudiri aniyar cikin ikon Allah a ƙarƙashin wannan shugabanci namu na riƙo za mu yi duk abin da za mu yi don ganin mun ɗora wannan ƙungiyar ta mu ɗoɗar akan hanya don ganin mun shiga cikin samun sauran ƙungiyoyin masu maganin gargajiya da ke jihohin ƙasar nan ta kowace fuska kuwa.”

“Shugaban ya kuma ba da tabbaci ga gwamnatin jihar ta Yobe cewar, za su bi dukkannin dokokin da gwamnatin ta gindaya ga masu maganin gargajiya don ganin mambobin ƙungiyar ba sa wuce gona da irin a yayin gudanar da wannan sana’a ta su ta maganin gargajiya kuma sun saba kayar ladabtar da duk wani mamban ƙungiyar da ya karya dokokin kungiya da kuma dokokin gwamnati.”

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Shugabannin soja na yankin Sahel suna gudanar da taro a Nijer, yayin da ECOWAS ke taro a Najeriya

Published

on

Shugabannin soja na yankin Sahel suna gudanar da taro a Nijer, yayin da ECOWAS ke taro a Najeriya

Shugabannin soja na yankin Sahel suna gudanar da taro a Nijer, yayin da ECOWAS ke taro a Najeriya

Afirka ta Yamma mai rarrabuwan kai ta gudanar da tarukan ƙolin shugabannin ƙasa guda biyu a ƙasashe daban-daban biyu a ƙarshen makon, inda aka gudanar da taro farko ranar Asabar a Nijar tsakanin shugabannin mulkin soja na yankin Sahel.
A gefe guda kuma za a gudanar da wani taron ƙoli ranar Lahadi a Najeriya inda shugabannin sauran ƙasashe mambobin ƙungiyar tattalin arziƙin yankin ta ECOWAS za su hallara.

Taron ƙolin da ake yi yau Asabar a Yamai babban birnin Jamhuriyar Nijar, zai kasance karo na farko tsakanin shugabannin sojojin sabuwar ƙungiyar haɗin kan yankin Sahel wato Alliance of Sahel States ko kuma AES.

Mali, Burkina Faso da Nijar su ne suka kafa yarjejeniyar kare juna a watan Satumba, waɗanda suka bar babbar ƙungiyar ECOWAS a cikin watan Janairu.

Ficewar su daga ECOWAS, wani ɓangaren ya samo asali ne daga zargin da suke yi cewa Paris tana yiwa ƙungiyar katsalandan kana ba ta ba da taimakon da ya kamata a yaƙi da masu iƙirarin yaƙin jihadi.

Ficewar ta sa ƙasashen uku sun janye kansu daga Faransa da ta yi musu mulkin mallaka, suka kori sojojin Faransa masu yaƙi da masu iƙirarin jihadin kana suka juya zuwa ga ƙasashen da suke ƙira da aminan gaskiya, da suka haɗa da Rasha da Turkiya da kuma Iran.

KU KUMA KARANTA:Shugabannin Nijar, Mali da Burkina Faso sun kafa ƙungiyar haɗaka

Idan aka yi la’akari da munanan tashe-tashen hankula na ‘yan jihadi da ƙasashen uku ke fuskanta, “yaƙin da ta’addanci” da “ƙarfafa haɗin gwiwa” za su kasance kan ajandar taron ƙolin na yau Asabar, a cewar fadar shugaban ƙasar Burkina Faso.

Taron ƙolin da za a gudanar ranar Lahadi a Abuja zai ba shugabanni a ƙasashen ECOWAS damar tattaunawa a kan irin alaƙa da za su ƙulla da ƙungiyar ta AES.

Bayan wasu tarurrukan da suke yi tsakanin ƙasashe biyu, shugabannin uku na yankin Sahel sun yi taro a karon farko tun bayan da suka hau karagar mulki ta hanyar juyin mulki tsakanin shekarar 2020 zuwa 2023.

Continue Reading

Labarai

Nan da 2030 za a fuskanci matsananciyar yunwa a Nijeriya — Majilisar Ɗinkin Duniya

Published

on

Nan da 2030 za a fuskanci matsananciyar yunwa a Nijeriya — Majilisar Ɗinkin Duniya

 

Nan da 2030 za a fuskanci matsananciyar yunwa a Nijeriya — Majilisar Ɗinkin Duniya

Majalisar Ɗinkin Duniya ta yi gargaɗin cewar ‘yan Najeriya miliyan 82, kimanin kashi 64 na ‘yan ƙasar ka iya fuskantar matsalar yunwa nan da shekarar 2030.

Haka kuma MƊD ta yi ƙira da gwamnatin ƙasar ta magance matsalar sauyin yanayi da matsalar ƙwari da sauran abubuwan da yi wa harkar noma barazana.

Jaridun Najeriya sun ambato jami’in Majalisar Ɗinkin Duniyar, Taofiq Braimoh – wanda ya wakilci kodinetan ayyukan jin ƙai na hukumar abinci da ayyukan noma na majalisar na bayyana haka lokacin da yake jawabi kan matsalolin ƙarancin abinci a taron ƙaddamar da shirin bunƙasa ayyukan noma na ‘CropWatch’ a birnin Abuja.

KU KUMA KARANTA:Majalisar Ɗinkin Duniya ta yi maraba da sakin yara 21 da aka yi garkuwa da su

Mista Braimoh ya ce akwai buƙatar gwamnatin Najeriya ta ɗauki matakan da suka dace cikin gaggawa don magance matsalar.

“Gwamnatin Najeriya tare da haɗin gwiwa masu ruwa da tsaki, sun gudanar da bincike na shekara-shekara da suka saba gudanarwa kan abinci. Sakamakon binciken ya tayar da hankali, kimanin mutum miliyan 82 ne za su fuskanci yunwa nan da 2030,” kamar yadda Jaridun ƙasar suka ambato Braimoh na bayyanawa.

Ya ci gaba da cewa matsalar rashin abinci da ƙasar ke fama da shi, baya rasa nasaba da matsalar sauyin yanayi da duniya ke fama da ita, da matsalar ƙwari da wasu abubuwa da ke yi wa harkar noma barazana a ƙasar.

Hasashen na Majalisar Ɗinkin Duniyar na zuwa ne a daidai lokacin da ƙasar ke fama da matsalar tsadar abinci, lamarin da ya tilasta wa gidaje da dama haƙura da sayen abincin da suka saba ci.

A cikin rahotonta baya-bayan nan, hukumar ƙididdigar ƙasar ta ce farashin abinci a ƙasar ya ƙaru zuwa kashi 40.66 a watan Mayu, matakin da aka jima ba a ga irinsa ba.

Continue Reading

Labarai

Yarjejeniyar Auren Jinsi: Gwamnatin Najeriya za ta kai jaridar Daily Trust kotu

Published

on

Yarjejeniyar Auren Jinsi: Gwamnatin Najeriya za ta kai jaridar Daily Trust kotu

Yarjejeniyar Auren Jinsi: Gwamnatin Najeriya za ta kai jaridar Daily Trust kotu

Daga Idris Umar, Zariya

Gwamnatin tarayyar Najeriya ta ce za ta maka jaridar Daily Trust a kotu, tare da shigar da ƙorafi game da ita, a gaban ƙungiyar masu gidajen jarida ta Najeriya saboda abin da ta ƙira ”yaɗa kalaman neman tayar da rikici da karya aikin jarida”

Ministan yaɗa labaran Najeriya, Mohammed Idris ya ce gwamnatin tana sane da yadda a cikin ‘yan watannin baya, jaridar Daily Trust ke yaɗa labaran da ke neman gogawa gwamnatin kashin kaji.

Da ya ke magana a wajen wani taron manema labarai a ranar Asabar, ministan yaɗa labaran ya kafa hujja da labaran da jaridar Daily Trust ta wallafa a game juyin mulkin Nijar, da wanda ya ce jaridar ta rubuta a kan shirin sauya sunan titin Murtala Muhammad da ke Abuja zuwa Wole Soyinka da kuma na baya bayan nan a game da sanya hannu a kan yarjejeniyar da ta shafi amincewa da auren jinsi.

KU KUMA KARANTA: Alaƙar soyayya tsakanin jinsi ɗaya ta haramta a Iraƙi

Ya yi bayanin cewa a dukkan labaran, gwamnatin ta gano yadda jaridar ta bayar da rahoto ba tare da gabatar da hujja ko shaidun zargin da ta yi ba, lamarin da kuma gwamnatin ke kallo a matsayin wani yunƙuri na wallafa ƙarya domin tunzura jama’a.

Ya ce: ‘’Ba mu taɓa tunanin Daily Trust da mutanen da ke da ita za su kai wannan mataki ba wajen neman tayar da rikici a ƙasar nan, ta hanyar zargin cewa gwamnati ta sanya hannu a kan yarjejeniyar tallata auren jinsi. Wannan tsabar zalunci ne saboda babu wannan tanadi a cikin yarjejeniyar.’’

Ministan ya koka da yadda wannan labarin ya janyo huɗuba mai zafi daga wasu malaman addini da kuma jefa jama’a cikin halin ɗarɗar, wanda kuma ya ce jaridar ce ta janyo.

KU KUMA KARANTA: Malaman addini a Malawi sun yi zanga-zangar nuna rashin amincewa da auren jinsi

Saboda haka, ministan ya ce ‘’Gwamnatin tarayya za ta bi duk hanyoyin da doka ta amince da su, domin neman haƙƙi a kotu.’’

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like