Connect with us

Labarai

Mutane bakwai sun mutu bayan sun sha shayi a wajen ɗaurin aure a Kano

Published

on

Mutane bakwai ne ake fargabar sun mutu, wasu da dama kuma sun kwanta a asibiti bayan sun sha shayin da ake zargin an yi shi da wani ganyen garin da aka fi sani da zaƙami a wajen wani ɗaurin aure a Kano.

Zaƙami yana ƙunshe da sinadari mai taɓa ƙwaƙwalwa.

Shedun gani da ido sun ce lamarin ya shafi kusan mutane 50 kuma har yanzu ba a gansu ba.

Lamarin ya faru ne a unguwar Sheka da ke ƙaramar hukumar Kumbotso a cikin birnin Kano.

Ɗaya daga cikin waɗanda suka shaida lamarin, Sanusi Yahaya, wanda kuma ɗan uwa ne ga amaryar, ya ce ana zargin shayin da wasu magunguna daban-daban banda ganyen gida.

KU KUMA KARANTA: Mutune 5 Sun Mutu, 10 Sun Bata A Wani Hari Da Aka Kai A Jihar Benue

Ya ce ya zama ruwan dare ga matasan yankin musamman masu shaye-shayen miyagun ƙwayoyi su riƙa dafa shayi a lokacin bukukuwa kuma suna fakewa a ƙarƙashinsa domin shan ƙwaya.

“Sun dafa shayin kuma su da kansu ba su san adadi da nau’in magungunan da ke ciki ba har wasu sun yi watsi da shi. Amma wasu daga cikinsu sun dage cewa dole ne su sha shayin, suna masu cewa ƙwaƙwalwar su na iya ɗauka.

“Bayan shan shayin, mutane biyu sun mutu, wasu sun murmure yayin da wasu ke kwance a asibiti,” in ji shi.

Wani shaida Abdullahi Muhammad ya ce ya zuwa ranar Talata mutane bakwai ne suka mutu. Ya ce wasu daga cikin waɗanda ke kwance a asibiti ba ’yan unguwar ba ne amma suna wucewa ne kawai suka yanke shawarar shan shayin.

“Ba mu san ainihin adadin ba a yanzu, amma da safe an tabbatar da mutuwar bakwai.

Wasu ma ba a gayyace su zuwa ɗaurin auren ba, sun zo ne domin su yi kwalliya su sha kwaya,” inji shi.

Ba a iya samun angon don jin ta bakinsa game da lamarin saboda an ce ya gudu tare da wasu.

Ƙoƙarin jin ta bakin kakakin rundunar ‘yan sandan Kano, SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya ci tura domin ba a samu lambarsa ba.

Har yanzu dai bai amsa saƙon da aka aike masa ba har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto.

1 Comment

1 Comment

  1. Pingback: Ɗan Najeriya da ya auri Ba’amurkiya, ya shiga aikin soja a Amurka | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like