Connect with us

Tattalin arziƙin ƙasa

Mun yi asarar Naira miliyan 531 na kuɗaɗen shiga bayan harin jirgin ƙasa daga Abuja zuwa Kaduna – NRC

Published

on

Manajan daraktan hukumar kula da zirga-zirgar jiragen ƙasa ta Najeriya (NRC), Fidet Okhiria, ya ce dakatar da zirga-zirgar jiragen ƙasa daga Abuja zuwa Kaduna cikin watanni biyar ya janyo asarar kuɗaɗen shiga na N531m. Da yake magana da manema labarai a Legas, Okhiria ya bayyana cewa adadin na wakiltar abin da za a iya samu ta hanyar siyar da tikitin jirgin ƙasan fasinja, wanda ‘yan ta’adda suka kai wa hari kimanin watanni shida da suka gabata.

Ya kuma ce gwamnatin tarayyar Najeriya ba za ta sake buɗe layin dogo ba har sai an sako sauran fasinjojin da ke hannun ‘yan bindiga.

Ya ƙara da cewa, kamfanin ya maido da na’urorin da suka lalace tare da gyara hanyar, amma aikin jirgin ƙasa ba zai koma ba, ya kara da cewa ma’aikatan jirgin ƙasa hudu na daga cikin waɗanda ake tsare da su.

“Gwamnati ta kafa wani kwamiti da zai tabbatar da mafi girman tsaro ga fasinjojin jirgin ƙasa da kayan aiki yayin gudanar da aiki. Mun yi imanin ya kamata a sanya matakan tsaro da suka dace kuma har sai lokacin, Gwamnatin Tarayya ba za ta amince da aikin tashar jirgin kasa ba.

“Ministan Sufuri yana jagorantar fafutukar ganin an sako wadanda ake tsare da su lafiya. Ba za mu iya tafiya da ƙarfi ba don tabbatar da cewa babu wanda ya rasa ransa. Muna magana ne game da fasahar zamani ta yadda za mu iya samun sa ido na gaske tare da tura jami’an tsaro da yawa don su kasance a wurare masu mahimmanci.

“Mun ziyarci IG, da ma’aikatar domin samun bayanai, kuma muna aiki tare don tabbatar da cewa ‘yan Najeriya sun tsira, ba masu amfani da jirgin ƙasa kadai ba. A duk lokacin da suka sako wasu, mu kan yi bincike a cikin takardar mu don tabbatar da cewa sunayensu ya bayyana sannan mu kai rahoto ga hukumar da ta dace.”

“Tun daga ranar 28 ga watan Maris da ‘yan ta’adda suka kai hari kan jirgin Abuja zuwa Kaduna, inda suka kashe mutane 8 tare da yin garkuwa da fasinjoji 62, bai ci gaba da aiki ba. Mun yi asarar N531m tsakanin ranar 28 ga watan Maris da harin jirgin ƙasa ya faru da watan Agusta ta hanyar sayar da tikitin tikitin jirgin da aka dakatar daga Abuja zuwa Kaduna,” in ji shi.

Shugaban NRC ya ce jirgin ƙasan Legas zuwa Ibadan yana tafiya sau hudu a kullum, kamar yadda sauran zirga-zirgar jiragen kasa na yau da kullun, ciki har da layin Warri-Itakpe.

2 Comments

2 Comments

  1. Pingback: Mun yi asarar Naira miliyan 531 na kuɗaɗen shiga bayan harin jirgin ƙasa daga Abuja zuwa Kaduna – NRC – LEGEND FM DAURA

  2. Pingback: Elon Musk ya zama mutum na farko a tarihi da ya yi asarar dala biliyan 200 | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Ra'ayi

Alherin janye tallafin manfetur, daga Auwal Mustapha Imam PhD

Published

on

Shi fa wannan lamari na janye tallafin da gwamnati ta yi a man fetur gabaɗayansa alheri ne ga talaka da Nigeria. Akwai raɗaɗi dai kafin a saba, amma idan an daure za a ga alherinsa. An daɗe ana siyasantar da lamarin cigaban Nigeria ne, shiyasa muka kasa gane tsare-tsaren da za su anfanemu da waɗanda za su cutar da mu.

Tun a lokacin mulkin Obasanjo aka so a cire tallafin man fetur, amma siyasa ta hana. An yi ta tallace-tallace a gidajen TV da radio don a wayar da kan talaka cewa “deregulation” a fannin man fetur shine mafita ga cigaban ƙasa Nigeria, amma an kasa aiwatarwa. Kowa tunaninsa idan ya aiwatar, ba lallai jam’iyyarsa ta ci zaɓe ba.

Gwamnati na kashe tiriliyoyin kuɗi wurin biyan tallafin man fetur da ake shigowa da shi domin a ɗauki man fetur ɗin a sauke a ko ina a Nigeria cikin sauƙi. To amma hakan ba mafita bane, domin kuɗin da ya kamata a yi wa Nigeria ayyukan cigaba su ne ake kashewa wurin biyan tallafin.

Jiya na ce, na samu ƙarin sama da Naira dubu ashirin (N20,000) a kan yadda na saba sayen mai. Kenan a duk lokacin da na saya man fetur, gwamnati na yi min cikon kuɗi. Motoci na guda biyu ne, kuma aƙalla na kan cika tankin kowace sau biyu a wata ɗaya. Kenan gwamnati na yi min cikon sama da Naira dubu ɗari a kowane wata. Abin tambaya shine, shin wanda bashi da mota shi ta ina gwamnati ke taimakonsa?

KU KUMA KARANTA: Cire tallafin mai: An tashi baran-baran tsakanin ƙungiyar ƙwadago da Gwamnatin Najeriya

Za ku iya cewa idan man fetur yayi sauƙi, talaka zai samu sauƙin kayan masarufi, to ai ni ma da kuma duk wanda ke da mota muna samun wannan sauƙin na kayan masarufi. Hanya ɗaya da gwamnati za ta samar da anfanuwa ga kowa shine a samar da hanyoyin sufuri masu inganci ga kowa, a samar da asibitoci da magunguna, a samar da makarantun boko masu kyau da Malamai masu nagarta. Duka waɗannnan ba za su samu ba, saboda babu wadatattun kuɗaɗe da za a yi haka.

Kuɗaɗen da ya kamata a samar da su, sune suke tafiya wurin biyan tallafin man fetur. Idan kun lura, man fetur ya fi tsada a duka sauran ƙasashen duniya da suka cigaba. Suna anfani da kuɗaɗen su wurin samar da cigaban ƙasa. Amma a Nigeria, ana karkatar da kuɗaɗen wurin biyan tallafin man fetur.

A baya, gwamnatin shugaba Jonathan ta rage tallafin, sai ta ƙirƙiro hukumar SURE-P da ta yi anfani da waɗannan kuɗaɗen da aka rage na tallafin domin aiwatar da ayyukan cigaban ƙasa da samar da walwala ga yan ƙasa. Tun a shekarar da ta gabata shugaba Buhari ya sanar da janye tallafin gaba ɗaya, sai koke-koke yayi yawa na matsanancin hali da ake ciki. Daga nan ne sukayi alƙawarin janye tallafin gaba ɗaya a watan June ɗinnan da muke ciki.

A taƙaice, duk da cewa Shugaba Tinubu na da niyyar cire tallafin gaba ɗaya idan ya amsa mulki kamar yadda ya sanar tun kafin ya ci zaɓe, amma ya zo ya tarar da kammalallen shirin na cire tallafin a wannan watan. Shiyasa ya jaddada shi.

Wani abu kuma da ya kamata mu sani shine, dilolin man fetur na anfani ne da wannan tallafin wurin cin amanar ƙasa Nigeria. Suna shigo da man fetur su nuna wa gwamnati, idan aka biya su kuɗin tallafin, sai su karkatar da man zuwa gidajen mai masu tsada. Kenan dakatar da tallafin mataki ne na hana almundahana a Nigeria.

Samun sauyin rayuwa na da zafi, amma idan an daure, za a ga anfaninsa. Musamman idan an gudanar da gwamnati da gaskiya da amana.

Daga ƙarshe, ina bada shawara kamar haka;

  1. A rage zirga zirgan da ba su zama dole ba.
  2. A ririta kuɗi ta hanyar kaucewa abubuwan da basu da muhimmanci.
  3. Idan za ku yi tafiya da motocinku, ku tsaya ku ɗauki passengers a tasha domin a rage kuɗin mai. Amma a kiyaye da ɗaukar ɓarayi.
  4. A riƙa tafiya a ƙasa zuwa inda ba zai gagara ba.

Idan muka ɗauki waɗannan matakan, za mu samu sauƙi sosai kafin mu saba.

Muna roƙon Allah ya bamu abin saya. Amin.

Auwal Mustapha Imam , Ph.D.

Continue Reading

Labarai

Kamfanin NNPC ya koma aikin nemo mai a jihar Borno

Published

on

Kamfanin mai na Najeriya NNPC ya sanar da komawa aikin neman mai a yankin Tafkin Chadi da ke jihar Borno.
Kamfanin ya dakatar da aikin ne a watan Yuli na shekara ta 2017, bayan da wasu mahara da ake zargin ‘yan Boko Haram ne suka kai wa ma’aikatan hari har suka yi garkuwa da wasu.
Shugaba Buhari ya gabatar da jawabi ta intanet ga taron ƙaddamar da komawa kan aikin gano man a wata rijiya da ke yankin Wadi-B a garin Tuba na ƙaramar hukumar Jere.

KU KUMA KARANTA: A watan Yuli za mu fara samar da man fetur – Ɗangote

Bayan da yanayin tsaro ya inganta ne a shekara ta 2022 kamfanin ya yanke shawarar sake komawa aikin a rijiyar ta Wadi-B. Jaridar daily Trust ta ruwaito cewa a lokacin da daraktan zartarwa na ɓangaren aikin neman man a kamfanin na NNPC, Mukhtar Zanna, ya ce za a toni rijiyar zuwa zurfin ƙafa dubu 14.

Ya ce suna da ƙwarin gwiwa a kan aikin saboda suna da bayanai da kuma sabuwar fasaha ta zamani.
Kamfanin ya ce yana da kyakkyawan zato cewa za a samu mai da gas mai yawan gaske a wannan wuri.

Continue Reading

Gwamnatin Tarayya

A watan Yuli za mu fara samar da man fetur – Ɗangote

Published

on

Shugaban rukunin Ɗangote, Alhaji Aliko Ɗangote ya bayyana cewa sabuwar matatar man Ɗangote da aka ƙaddamar za ta samar da kason farko na albarkatun man fetur ga kasuwa kafin ƙarshen watan Yuli.

Attajirin ɗan kasuwar nan na Najeriya ya bayyana haka ne a ranar Litinin ɗin da ta gabata a wajen bikin ƙaddamar da aikin matatar man, mai 650,000 a kowace rana (BPD), aikin haɗaka da matatar mai da ke yankin Lekki na yankin ciniki maras shinge na jihar Legas.

Haɗin matatar man fetur da rukunin sinadarai za su samar da ayyukan yi kai tsaye dubu 9,500 da kuma wasu 25,000. Da yake jawabi a wurin bikin, Ɗangote ya ce bikin ƙaddamar da wani sabon salo ne mai ƙayatarwa ga ɓangaren mai da iskar gas na Najeriya.

KU KUMA KARANTA: Hamshaƙin ɗan kasuwa Ɗangote, ya gina babbar matatar mai a Najeriya

Ya ce: “Akwai ƙwarin guiwarmu cewa za mu kwaikwayi a wannan fanni abin da a zahiri muka samu a kasuwannin siminti da takin zamani yayin da Najeriya ta sauya daga kasancewar ta kan gaba wajen shigo da waɗannan ɗanyen kayayyaki zuwa masu fitar da kayayyaki zuwa ƙasashen waje.

“Manufarmu ta farko ita ce, mu zage damtse hasashen samar da kayayyaki iri-iri domin tabbatar da cewa a cikin wannan shekarar, mun samu damar biyan buƙatun al’ummarmu na samar da ingantattun kayayyaki, don ba mu damar kawar da bala’in dogaro da shigo da kayayyaki daga ƙasashen waje, mu daina gaba ɗaya. Ya zama a kasuwanninmu na kayayyakin mai da ba su da inganci.

“Kayan mu na farko za su kasance a kasuwa kafin karshen watan Yuli, farkon watan Agustan wannan shekara. “Kamfanin zai tabbatar da cewa ana sarrafa da gudanar da mafi girma da ƙarfi na mai, me amfani da inganci don baiwa matatar damar yin gasa da kasuwannin mai.”

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like