Connect with us

'Yansanda

Matashi ya bayyana shi ya shaƙe mahaifiyarsa har lahira saboda ta kira shi da shege

Published

on

Wani matashi ɗan shekara 18, Tope Momoh, ya amince ya shaƙe mahaifiyarsa mai shekaru 52, Stella, saboda ta kira shi da shege.

Momoh ya ce ya yanke shawarar amsa laifin da ya aikata bayan sati biyu da binne mahaifiyarsa saboda ya kasa samun sukuni da kwanciyar hankali. A cewar jaridar The Nation, an ce ya aikata laifin ne da tsakar daren ranar 6 ga Satumba, 2022, a Ikakumi Akoko, a jihar Ondo.

An gurfanar da Momoh a gaban wata Kotun Majistare ta Akure bisa tuhumarsa da laifin kisan kai kuma ya nemi a yi masa rahama. Ɗan sanda mai shigar da ƙara, Nelson Akintimehin, ya shaida wa kotun cewa ba a san musabbabin mutuwar mahaifiyar ba har sai da ɗanta ya amsa cewa shi ne ya kashe ta.

“Momoh a cikin ikirari nasa ya ce an tilasta masa ya shaida wa ‘yan uwansa cewa ya shaƙe mahaifiyarsa har lahira. Hakan ya faru ne lokacin da ta tada shi da tsakar dare, inda ta yi masa ruwan tsinuwa tare da kiran sa da shege.

“Akintimehin ya ce laifin ya ci karo da sashe na 319(1) na kundin laifuffuka, Cap 37, Vol. II Dokar Jihar Ondo, 2006. Momoh, a sanda aka basa izinin yin magana yace, “Ni ban samu nutsuwa ba tunda aka binne mahaifiyata. Don haka, ya zamar min dole in furta cewa ni na shaƙe ta har ta mutu. Don haka ina so kotu ta tausaya mani.”

Ba a sauƙaka masan ba, amma Alƙalin kotun, Musa Al-Yunnus, ya bayar da umarnin tsare shi a gidan gyaran hali na Olokuta sannan ya dage sauraron karar zuwa ranar 20 ga Oktoba, 2022.

Click to comment

Leave a Reply

'Yansanda

‘Yan sanda sun kama wani ɓarawon mota

Published

on

'Yan sanda sun kama wani ɓarawon mota

‘Yan sanda sun kama wani ɓarawon mota

Daga Ali Sanni Larabawa

Rundunar ‘yan sandar babban birnin tarayyar Najeriya, sunyi nasarar kama wani mutum da ake zargi da ƙwace wata mota ta hanyar amfani da bindiga, watanni uku da suka wuce.

Kwamishinan ‘yan sandar Abuja, Benneth Igweh ne, ya bayyana hakan lokacin da yake gabatar da wanda ake zargi a ranar Litinin.

Ya ce wanda ake zargin, mai suna Michael Uke, ya sace mota ƙirar Toyota Corolla mai lamba ABC 258 LD ta hanyar amfani da bindiga a ranar 2 ga watan Mayu, 2024, a kan hanyar Kuje.

KU KUMA KARANTA: Wasu matasa a Bauchi sun ƙone ɓarayin adaidaita sahu har lahira

‘Yan sandan sun bi sawun sa har zuwa wani otal dake yankin Jabi, inda suka same shi tare da motar daya sace.

‘Yan sandan sun kuma gano cewa wanda ake zargin ya sauya lambar motar zuwa AGD 146 JP.

A yayin binciken, sun gano na’urar POS, wuƙa, da kuma hular sojoji a wajensa.

‘Yan sandan na cigaba da gudanar da bincike  a kan lamarin.

Rundunar ta buƙaci mazauna yankin su riƙa sanar da su abubuwan da ke faruwa ta waɗnnan lambobin: 08032003913, 08028940883, 08061581938, da 07057337653.

Continue Reading

'Yansanda

‘Yan sanda sun kama matashin da ake zargi da yin garkuwa da ‘yar maƙocinsa

Published

on

'Yan sanda sun kama matashin da ake zargi da yin garkuwa da 'yar maƙocinsa

‘Yan sanda sun kama matashin da ake zargi da yin garkuwa da ‘yar maƙocinsa

Daga Shafaatu Dauda,Kano

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano, ta kama wani matashi mai suna Zakariyya Muhammad, da ake zargi da laifin yin garkuwa da ƙaramar yarinya mai shekaru biyu da rabi.

Kakakin Rundunar ‘yan sandan jihar Kano, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ne ya bayyana hakan ta cikin wata sanarwa da ya aike wa da manema labarai a ranar Talata.

Sanarwar ta ce, tun a Ranar 4 ga watan Yuli 2024, rundunar ta samu ƙorafi daga wani Mazaunin unguwar Sabuwar Gandu Kwarin Barka, cewar wani ya ƙira wayar sa inda ya shaida masa cewar ya yi garkuwa da ‘yarsa mai suna Amina , har aka nemi a biya shi kuɗin fansa naira miliyan biyu kafin ya sake ta.

Bayan samun korafin ne Kwamishinan ‘yan sandan jihar Kano, CP Salman Dogo Garba, ya tayar da dakarun ‘yan sanda ma su yaƙi da garkuwa da mutane, ƙarƙashin jagorancin SP Aliyu Muhammad Auwal, tare da ba Su umarnin kuɓutar da yarinyar cikin a wanni 24, da kuma kama waɗanda ake zargin.

SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya ƙara da cewa, an yi nasarar kama wanda ake zargin Zakariya Muhammad , a ranar 5 ga watan Yuni 2024, inda ya tabbatar da cewar shi ne ya yi garkuwa da yarinyar sannan ya nemi kuɗin fansa.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan sanda a Kano sun ceto ’yar shekara 2 da maƙocinsu ya sace

Neptune Prime Hausa ta kawo rahotan na cewa tuni aka kuɓutar da yarinyar kuma likitoci sun tabbatar da cewar kalau ta ke.

Kakakin Rundunar ‘yan sandan Kano, ya ce an dawo da batun babban sashin binciken manyan laifuka dake Bomapai, ɓangaren da ya shafi garkuwa da mutane, kuma da zarar an kammala bincike za a gurfanar da shi a gaban kotu.

Rundunar ta ja hankalin iyaye su dinga kula da ‘ya’yansu, tare da jan kunnen matasa cewar wannan ba abin yi ba ne, kuma ba sana’a ba ce, musamman a jihar Kano domun ma su yunƙurin aikata ba su da wajen ɓuya.

Continue Reading

'Yansanda

An ja hankalin ‘yan Najeriya kan shirin ƙungiyoyin asiri na ɗaukar sabbin mambobi

Published

on

An ja hankalin 'yan Najeriya kan shirin ƙungiyoyin asiri na ɗaukar sabbin mambobi

An ja hankalin ‘yan Najeriya kan shirin ƙungiyoyin asiri na ɗaukar sabbin mambobi

Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta ja hankalin ‘yan ƙasar game da shirin ƙungiyoyin asiri na ɗaukar sabbin mambobi a faɗin ƙasar musamman a jami’o’i da manyan makarantu.

Mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan Najeriya reshen Jihar Ribas Grace Iringe-Koko ce ta yi wannan jan hankali a cikin wata sanarwa da ta fitar ranar Asabar da maraice a birnin Fatakwal.

Ta bayyana cewa wata babbar ƙungiyar asiri ta Najeriya tana shirin gudanar da gagarumin biki ranar Lahadi a faɗin Najeriya, musamman a jami’o’i don tunawa da mutumin da ya kafa ta.

“Rundunar ‘yan sandan Jihar Ribas ta samu bayanai game da bikin da ƙungiyar Neo-Black Movement (NBM) za ta yi a faɗin ƙasar ranar 7 ga watan Yulin 2024. Ƙungiyar, wadda ake yi wa laƙabi da Aiye ko Black Axe, tana shirin gudanar da bikin ne domin tunawa da wanda ya kafa ta.

KU KUMA KARANTA: Shugaban hukumar leƙen asirin sojin Isra’ila ya yi murabus saboda harin Hamas na 7 ga Oktoba      

Bikin, wanda aka sanya wa suna Ranar AIYE ko 7/7 za a gudanar da shi ne a dukkan jihohin da ke faɗin ƙasa, musamman a manyan makarantu,” in ji sanarwar.

An gargaɗi masu ta da hankalin jama’a a Bikin Dodanni na Egungun a Jihar Oyo

Rundunar ‘yan sandan ta ce tana sane da munanan ayyukan ƙungiyar asirin na kisan mutane a manyan makarantu da faɗace-faɗace a tsakanin ƙungiyoyin asiri da tayar da zaune-tsaye da sauran manyan laifuka.

Ta ce yanzu haka ta baza ƙarin jami’an ‘yan sanda zuwa wasu wurare domin daƙile ayyukan ƙungiyoyin asiri, sannan ta yi ƙira ga iyaye su gargaɗi ‘ya’yansu su guji shiga ayyukan ƙungiyoyin asiri.

“Ana bai wa manyan makarantu shawarar ƙara matakan tsaro da kuma sanya idanu sosai domin tabbatar da tsaron dukkan ɗalibai.

Kazalika ana ƙira ga dukkan makarantu su lura da duk wani taro na ɗalibai da bai kwanta musu a rai ba,” a cewar sanarwar.

Continue Reading

You May Like