Connect with us

Labarai

Matar Marigayi Abba Kyari ta zama Gimbiya ta farko ta Masarautar Jama’are

Published

on

Sarkin Jama’are, Alhaji Nuhu Muhammadu Wabi, a ranar Lahadi ya naɗa matar tsohon shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa Muhammadu Buhari, marigayi Abba Kyari, Hajiya Hauwa Kulu Abba Kyari a matsayin ‘Gimbiya ta Jama’are’ ta farko. Da yake jawabi a wajen bikin rawani a fadarsa, Sarkin Jama’are, Nuhu Muhammadu Wabi ya bayyana ta a matsayin ‘yar Jama’are ta gaskiya wadda ta yi ƙoƙari wajen ci gaban Masarautar baki daya.

A cewar Sarkin, aikin Gimbiya na gargajiya shi ne ya zama wata gada tsakanin Sarki da matan da ba su da ra’ayin kai tsaye a cikin al’amuran gargajiya, “Tare da rawani a matsayin Gimbiya, matan Jama’are yanzu sun samu wakilai a Majalisar Masarautar, yanzu ana iya jin muryoyinsu ƙarara”.

“Na cika cewa a yanzu ina da ‘yar Masarautar ta gaske a Majalisar, mace ce mai zuciya da ta damu da jin dadin jama’arta da kuma ci gaban masarautar,” inji shi. Sarkin ya ce, “Duk da cewa ta bayar da gudunmawar abubuwa da dama wajen ci gaban Masarautar Jama’are, da wadannan muna sa ran fiye da haka, wannan shi ne aikin da ke wuyanta a yanzu”.

A taƙaitaccen jawabin da ta yi bayan an yi rawani, Gimbiya ta farko ta Jama’are, Hauwa Kulu Abba Kyari ta gode wa Sarkin bisa yadda ya same ta da wannan karramawa wanda ya zo mata da mamaki.

Ta jaddada ƙudirinta na ci gaba da bayar da gudummawar kasonta don ci gaban Masarautar da jama’ar Jama’are wadanda ta ce sun yi tasiri sosai a rayuwarta, ta kuma nuna farin cikinta da karramawar da akai mata, wanda tace yazo mata ne ba tsammani.

A martanin da ya mayar dangane da wannan rawani, Manajan Daraktan Rukunin Kamfanin na NNPC, Mele Abba Kyari ya yi mata fatan alheri inda ya ce kira ne a gare ta da ta ƙara himma wajen ci gaban Masarautar Jama’ar da kuma bil’adama baki daya. “Muna nandin taya ‘yar’uwar da ta yi kyakkyawan aiki ga bil’adama kuma ta cancanci a gane haka”.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like