Connect with us

Al'ajabi

Matar da ke tunƙaho da gashin-bakinta

Published

on

Daga Fatima GIMBA, Abuja

Masu ziyartar shafukan sada zumunta da muhawara na nuna sha’awa da kuma yabo yayin da wasu ke nuna kyama ga wata mata ‘yar Indiya wadda ke da baiwar gashin-baki.

Sai dai duk da yadda wasu ke mata zambo da shaguɓe ita kam ta ce ko a jikinta, hasali ma tana son wannan baiwa ta fuskar tata.

Shyja

Shyja mai shekara 35 ta rubuta a shafinta na WhatsApp bangaren hotonta cewa, ”Ina ƙaunar gashin-bakina.”

Yawancin mutanen da suka hadu da ita a Facebook ko kuma suka ganta a zahiri sukan tambaye ta dalilin da ya sa take barin gashin-bakin, har ma take ado da shi.

“Abin da nake gaya wa mutane kawai, shi ne, ina son abuna sosai,” in ji ta.

Shyja, wadda ke amfani da suna daya kawai tana zaune ne a gundumar Kannur a jihar Kerala da ke arewacin kasar ta Indiya.

Harnaam Kaur, me fafutuka ‘yar Birtaniya ta faɗa tana gwagwarmaya kan barin kowa yayi adon ji jikinsa yadda yakeso

Ita ma kamar sauran wasu mata ta dade da wannan gashin-baki.

Duk da cewa tana rage girarta akai-akai, Shyja ta ce, ita ba ta taba tunanin wai ta aske gashin-bakinta ba.

Kusan shekara biyar da ta wuce sai gashin ya riƙa fitowa sosai kamar na namiji, wanda hakan ya ba ta sha’awa sosai, har ma ta ce bari ta bar shi kamar yadda na maza yake.

”Bana ma taɓa tunanin yadda zan ci gaba da rayuwa ba tare da wannan gashin-bakin ba.

Lokacin da aka fara annobar korona, ba na son sanya takunkumi kodayaushe saboda yana rufe min fuska,” in ji ta.

Mutane da yawa idan suka ganta sai su ce mata ta aske shi, amma ta ƙi.

Ta ce, ”Ban tana jin cewa ni ba kyakkyawa ba ce saboda ina da wani abu da bai kamata a ce ina da shi a jikina ba.”

“Yawanci ana gaya wa mata cewa bai kamata su bar gashi a fuskarsu ba, na shawartarsu da su je su biya a aske musu ko kuma a gyara musu shi yadda zai yi kyau kodayaushe,” in ji ta.

Akwai mai da sauran abubuwa na aske ko fitar da gashi ko kuma gayra shi masu tsada, wadanda musamman na mata ne wadanda a su iya saye.

To amma a ‘yan shekarun nan mata da yawa sun yi watsi da wannan al’ada ta aske gashin da ke fitowa a wani sashe na fuskarsu, har ma alfahari suke yi da shi.

A shekara ta 2016, mai rajin kare ‘yancin gyara jiki Harnaam Kaur ta kasance matashiyar mace ta farko a duniya da ta tsayar da gemu cikakke kamar namiji, in ji littafin tattara bajinta na duniya (Guinness World Records).

A wajen Shyja, barin gashin-baki ba wai nuna wata manufa ba ce, illa kawai halitta ce da jikin mutum yake da ita, wadda za a gani a san yadda kake.

Ta ce “Ni ba abin da ya dame ni ina rayuwata ne yadda nake so Idan da rai biyu gare ni, da watakila sai na bar wa wasu su yi daya rayuwar.”

Wasu daga cikin irin wadannan abubuwan suna samun mutum ne idan ya gamu da larura ta tsawon shekaru.

An yi wa Shyja tiyata har sau shida a cikin shekara goma – daya an fitar mata wani kumburi ne a nononta, wata kuma an cire mata wani kari ne a mahaifarta.

Tiyata ta karshe da aka yi mata shekara biyar da ta gabata, an cire mata mahaifa ne.

“Duk lokacin da aka fito da ni daga dakin tiyata, fata nake a ce ba za a sake shiga da ni ba,” in ji ta.

Ganin bayan matsaloli na lafiya iri daban-daban ta Shyja ta yi ba abin da hakan ke sa ta sai dai samun kwarin guiwa na ta yi rayuwarta yadda take so.

Shyja ta ce tana da kunya sosai lokacin tana ‘yar karama.

Ba kasafai ake ganin mata a waje ba a kauyensu bayan karfe shida na dare.

Duk da cewa Kerala na daya daga cikin jihohin Indiya da suka fi ci-gaba, to amma har yanzu al’adar maza su mamaye komai ita ake yi a yawancin wurare.

Kuma galibi ba a son mata su rika tafiye-tafiye ko kuma zama su kadai.

Lokacin da ta yi aure ta koma jihar Tamil Nadu, mai makwabtaka da su, Shyja ta ce sai ta ji dadin irin rayuwar da ta samu kanta a ciki.

Kamar ta samu wani sabon ‘yanci da walwala.

“Mijina zai tafi aiki sai can dare zai dawo. Saboda haka da yamma sai in fito kofar gida na zauna. Wani lokaci ma sai na je shago ni kadai da daddare na sayo kaya idan ina bukata.

Ba wanda ya damu. Yadda ya kasance na fara yin abubuwa ni kaɗai, abin ya sa na samu kwarin guiwa a rayuwata.”

Ta kara da cewa, ” Yanzu irin wannan al’ada nake so na koya wa ‘yata.”

Iyaye da dangi da kuma kawayen Shyja suna ba ta goyon baya a kan son gashin-bakin da take yi.

A lokuta da dama ‘yarta kan ce mata gashin-bakin ya yi mata kyau.

Amma kuma Shyja ta ce ba irin maganganun da mutane ba sa gaya mata idan suka hadu da ita a titi.

“Mutane na yi min dariya, suna cewa ‘maza ne da gashin-baki, ya mace kuma take da shi?'” in ji ta.

A shekarun baya, a lokuta da dama an yi ta nuna ta da yin rahoto da shiri a kanta a kafafen yada labarai na kasar.

A baya-bayan nan, ta ce ta ga maganganu da sakonni da aka yi ta yi a kan wata makala da aka rubuta a kanta.

Ra’ayoyin da wata kafar yada labarai ta sanya a shafinta na Facebook.

Wani daga cikin masu bayyana ra’ayin nasu, ya ce, ”Me ya sa ba za ta aske gashin-bakin nata ba, tun da har tana dan aske girarta ta gyara ta.

“To amma wannan ba ra’ayina ne na barin abin da nake so a jikina da kuma abin da bana so ba?” Ta tambaya.

Yawanci kawayen Shyja suna mayar da kakkausan martani a kan wadannan ra’ayoyi na Facebook, amma ita cewa take abin ba ya damunta ko kadan.

“Hasali ma wani lokaci kallonsu kawai nake na yi dariya.”

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Al'ajabi

An ƙona mutane suna Sallar Asuba a masallaci a Kano

Published

on

An ƙona mutane suna Sallar Asuba a masallaci a Kano

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano a arewacin Najeriya ta ce ta kama wani mutum da ake zargi da cinna wa wani masallaci wuta yayin da mutane ke Sallar Asuba ranar Laraba.

Lamarin ya faru ne a ƙauyen Gadan da ke Ƙaramar Hukumar Gezawa a jihar ta Kano, da misalin karfe 5:20 lokacin da ake sallah, a cewar sanarwa ‘yan sanda.

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Kano, Abdullahi Haruna Kiyawa ya tabbatar wa da TRT Afrika Hausa faruwar lamarin da kama mutumin da ake zargi, sai dai ya ce ana ci gaba da gudanar da bincike.

Abdullahi Kiyawa ya ce bincike ya nuna cewa mutumin da ake zargi da cinna wutar Shafi’u Abubakar mai kimanin shekaru 38 ya jefa wata roba ne ɗauke da fetur cikin masallacin, sannan ya cinna wuta.

KU KUMA KARANTA: Mahara a Anambara sun ƙona fadar babban Basarake ƙurmus

Kakakin ‘yan sandan ya ce mutum 24 ne suka ƙone a masallacin, da suka haɗar da manya 20, yara huɗu.

An garzaya da duka waɗanda suka jikkata zuwa asibiti don ba su kulawa, amma babu wanda ya mutu a haɗarin, a cewar sanarwar ‘yan sandan.

Continue Reading

Al'ajabi

An tsinci gawar wata ɗaliba a cikin ɗaki a Kano

Published

on

An tsinci gawar wata ɗaliba mai suna Aisha Yahaya ta Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Aliko Ɗangote da ke Wudil, a wani gida da ke wajen jami’ar.

Aisha, ɗaliba ce da ke matakin karatu na uku wato ‘level 300’ a sashen nazarin Kimiyya da Fasahar Abinci na jami’ar wadda aka tsinci gawarta bayan ta koma ɗakinta.

An ce ɗalibar ta rubuta jarrabawarta ta farko a zangon karatun na farko da ake yi a jami’ar.

Wasu daga cikin abokan karatunta sun danganta mutuwarta da shiga cikin matsi da damuwa a dalilin karatu da kuma zana jarrabawar.

A cikin wasiƙar ta’aziyyar, hukumar jami’ar ta bayyana matuƙar baƙin cikinta dangane da rasuwar Aisha Yahaya.

KU KUMA KARANTA: An tsinci gawar wani mutum a kan titi a Kano

Sanarwar ta ce, “Aisha ɗaliba ce mai hazaƙa wadda ta rasu a dalilin bugun zuciya. Za a riƙa tunawa da ita a kan sha’awarta na karatu da jajircewarta kan harkokin karatunta.”

Jami’ar ta ƙara da cewa, ba a iya gano wata da ke tattare da ita ba gabanin mutuwarta saboda ba ta nuna alamun rashin lafiya ko fama da wata cuta ba.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like