Connect with us

NAHCON

Maniyyatan jihar Kaduna za su biya kuɗin kujerar hajji cikin wata biyu

Published

on

Manniyyatan aikin Hajji daga Jihar Kaduna za su biya kafin-alƙalamin Naira miliyan biyu da dubu ɗari biyar, sannan su biya cikon miliyan biyu kafin ƙarshen watan Disamba.

Hukumar jin daɗin alhazai ta jihar Kaduna ta ba wa maniyyatanta wa’adin ranar 30 ga watan Disamba 2023 su kammala biyan cikon kuɗin kujerar aikin Hajji mai zuwa.

Hukumar ta umarci maniyyatan su biya Naira miliyan 2.5 a matsayin kafin alƙalami, sannan su biya cikon Naira miliyan biyu kafin cikar wa’adin.

Ta bayyana cewa za ta ba da fifiko da maniyyatan da ba su taɓa sauke farali ba wajen yin rajista, amma ba za ta amince da biyan kuɗin kujerar a bisa wakilci ba.

KU KUMA KARANTA: Maniyyata aikin Hajjin 2024 za su biya miliyan huɗu da rabi – NAHCON

Duk wanda aka maye gurbinsa a kujerar aikin Hajjin da ya biya kuma, to ba za a dawo masa da kuɗinsa ba, sai an kammala dawo da alhazai daga ƙasa Mai Tsarki.

Ta ce ɗaukar matakin ya zama dole saboda yadda wasu ke biyan kuɗin kujerar ba da niyyar su tafi ba, sai don daga baya su sayar wa waɗanda ba su samu ba da tsananin tsada.

Hukumar ta ce duk wanda ta gano ya yi haka to ba za ta amince ta maye gurbinsa ba, inda ta garagaɗi maniyyata su guji biyan kuɗi ta hannun jami’anta, su biya kai tsaye a banki sannan su kai takardar shaidar biyan kudinsu ga jami’an Hajji da ke kula da ƙananan hukumominsu.

Hukumar Aikin Hajji ta ƙasa (NAHCON) ta sanya Naira miliyan 4.5 a matsayin kuɗin kujerar aikin Hajjin na 2024.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Hukumar Alhazan Nijeriya ta ƙaryata zargin bai wa mahajjata abinci kaɗan

Published

on

Hukumar Alhazan Nijeriya ta ƙaryata zargin bai wa mahajjata abinci kaɗan

Hukumar Alhazan Nijeriya ta ƙaryata zargin bai wa mahajjata abinci kaɗan

Hukumar Alhazan Nijeriya NAHCON, ta ƙaryata wani labari da ake ta yaɗawa a shafukan sada zumunta da ake zarginta da bai wa mahajjata abinci ɗan kaɗan.

A ranar Talata ne aka fara yaɗa hoton nau’in abincin karin kumallo da ke nuna kunu kaɗan a wani mazubi da kuma ƙosai ƙwaya uku, inda aka ce wani ɗan jarida ne ya fara yaɗawa don nuna wa duniya yadda ake “bai wa mahajjata abinci kaɗan bayan biyan naira miliyan takwas kuɗin kujerar ajji.”

Lamarin ya jawo Allah wadai a shafukan intanet a Nijeriya, inda aka dinga zargin hukumar da “son wulaƙanta alhazai” kan irin nau’in abincin da take ba su duk da makuɗan kuɗaɗen da suka biya.

Sai dai a sanarwar da ta fitar a ranar Talata da marece mai ɗauke da sa hannun Hajiya Fatima Sanda Usara, mai magana da yawun NAHCON, ta ce “an jawo hankalinmu kan wani labarin ƙarya da shafin Facebook na wani Babagana Digima ya wallafa, da ke nuna wani nau’in abinci da aka ce shi muke raba wa alhazan Nijeriya bayan da suka biya kuɗin kujerar Hajji har naira miliyan takwas.”

KU KUMA KARANTA: Rukunin farko na Alhazan Kano sun tashi zuwa Saudiyya

“Bayan yin abin da ya dace a kan labarin daga tushe mun yi imani cewa dokokin watsa labarai ba su yarda ɗan jarida da ya san abin da yake yi ya dogara da labari daga Facebook kaɗai ba.

Wani abin takaici shi ne cewa ɗan jaridar da ya ɗauki labarin daga Facebook yana nan a Nijeriya bai je Saudiyyan ba,” in ji sanarwar.

NAHCON ta ce da samun labarin ba ta yi ƙasa a gwiwa ba sai ta ja hankalin wanda ya fara ƙirƙirarsa a fili da a bayyane kan rashin sahihancin ikirarin nasa inda ta nemi ya janye zargin, tana mai yi masa uzurin ko bisa rashin sani ya wallafa, amma sai ya ƙi yin hakan.

“Duk da haka alhazai da dama da suke Makkah a halin yanzu sun yi ta ƙaryata zargin nasa ta hanyar wallafa hotunan ainihin abincin da ake ba su a ƙasan labarin da ya wallafa, sannan ma’aikatan NAHCON ma da suke can sun yi bayanin irin abincin da ake bayarwa, suna masu cewa hoton da ya saka din an yi masa kwaskwarima ne, kuma ƙarya ce tsagwaronta.

“Amma duk da haka gidan jaridar Sahara Reporters sun yi biris da hakan.

Kuma jaridar ta yi amfani ne kawai da wani hoto na mahajjatan Babban Birnin Tarayya na abin karyawar da aka ba su a otel ɗinsu a Makkah, amma sai aka yi masa kwaskwarima aka wallafa shi.

A ƙarshe hukumar Alhazan ta yi ƙira ga al’umma da su yi watsi da labarin ƙaryar da ake watsawa a kan batun abin karyawar tana mai nanata cewa ƙarya ce da son ɓata mata suna.

Continue Reading

Labarai

Hukumar Alhazan Najeriya NAHCON ta ƙara kuɗin kujerar aikin Hajjin 2024

Published

on

Hukumar Alhazan Najeriya NAHCON ta ƙara farashin kujerar Aikin Hajjin bana da miliyan N1,918,032.91, inda ta bai wa maniyyata wa’adin zuwa 28 ga watan Maris ɗin 2024 su biya cikon kuɗin.

Mai magana da yawun hukumar Fatima Sanda Usara ce ta tabbatar da hakan a wata sanarwar da ta fitar a ranar Lahadi.

Hukumar ta NAHCON ta ce an samu wannan ƙarin ne sakamakon ƙaruwar farashin dala a Najeriya.

A baya dai NAHCON ta saka kuɗin Aikin Hajjin bana kan Naira miliyan 4.9, lamarin da ya sa aka yi ta kokawa da hakan.

KU KUMA KARANTA: NAHCON ta sanar da yadda Saudiyya ta rage kuɗin aikin Hajjin bana

Sai dai a halin yanzu ana buƙatar waɗanda suka biya kafin alƙalamin na miliyan 4.9 su biya ƙarin miliyan 1.9, wanda hakan ya kai jumullar kuɗin kowane maniyyaci zuwa miliyan 6.8.

Haka kuma hukumar ta bai wa maniyyatan zuwa 28 ga watan Maris su biya wannan cikon.

Sai dai a wani ɓangaren kuma hukumar ta sanar da cewa duk wani sabon maniyyaci daga arewacin Najeriya wanda yake son biyan kuɗin kujera a yanzu zai biya N8, 254, 464.74.

Sai kuma sabbin maniyyata daga jihohin Adamawa da Borno za su biya N8,225, 464.74 sai kuma ƴan kudancin Najeriya za su biya N8, 454, 464.74.

Continue Reading

Labarai

NAHCON ta sanar da yadda Saudiyya ta rage kuɗin aikin Hajjin bana

Published

on

Hukumomi a ƙasar Saudiyya sun yi ragin kuɗin Hajji ga maniyyatan da za su sauƙe farali a bana, 2024, domin farantawa mahajjata.

Hukumar Aikin Hajji ta Ƙasa (NAHCON) ta sanar cewa shugabata, Jalal Ahmad Arabi, ne ya nemo ragin da aka yi, wanda ya shafin kuɗin tikitin jirgi, masauki, jigila da sauran hidimomin da ake wa alhazai a Saudiyya.

Mai magana da yawun hukumar NACHON, Fatima Sanda Usara ce ta sanar da hakan a ranar Laraba, inda ta ce a sakamakon haka, Saudiyya ta rage “Dala 138 daga kuɗin tikitin jirgin da aka biya a 2023, masauki a Madina daga Riyal daga 2,080 ya koma 1,665, masauki a Makkah ya koma Riyal 3,000 daga 3,500.

KU KUMA KARANTA: NAHCON ta ba maniyyata aikin hajjin baɗi mako uku su fara biyan kuɗaɗensu

“Zama a Muna da Arafa da Muzdalifa kuma an rage shi zuwa Riyal 5,393 zuwa 4,770,” in ji ta.

Sai dai duk da haka, sanarwar ba ta bayyana ko NAHCON za ta yi wa maniyyayatan Najeriya ragin kuɗin kujera daga naira miliyan 4.5 da ta sanar tun da farko ba.

Kazalika ana hasashen duk da sauƙin da wannan Saudiyya ta yi, da wuya maniyyayatan Najeriya su shaida sauƙin — daga naira miliyan 3 da suka biya a 2023 — sakamakon tashin farashin Dala.

Farashin kuɗaɗen ƙasashen waje musamman Dala sai ƙara ƙaruwa yake a Najeriya, lamarin da ke ƙara haifar da tsadar rayuwa a ƙasar.

Akasari ana biyan kuɗin aikin Hajji da sauran huldodin ƙasa da ƙasa, kamar aikin Hajji da sauransu ne da Dala ko sauran kuɗaɗen ƙasashen waje.

Faɗuwar darajar kuɗin Najeriya, naira da tashin dala da danginsa a ƙasar ta sa a duk shekara kuɗin aikin Hajji ƙaruwa.

A sakamakon haka ne aka samu ƙarin kashi 50 a kuɗin aikin Hajjin 2024 a kan na 2023.

Rahotanni sun bayyana cewa an samu raguwar maniyyayatan Najeriya da za su sauƙe farali a bana a sakamakon tsadar kuɗin kujera.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like