Connect with us

Labarai

Maharan jirgin ƙasan Abuja zuwa Kaduna sun sako wasu fasinjoji 7 da suka sace

Published

on

Daga Fatima GIMBA, Abuja

Bakwai daga cikin fasinjojin da aka yi garkuwa da su a harin da aka kai kan jirgin ƙasa a jihar Kaduna ranar 28 ga Maris, sun sami ‘yanci.

An sako mutanen bakwai ne a safiyar Laraba bayan da suka shafe kwanaki 135 a hannun ‘yan ta’addan.

Tukur Mamu, mawallafin Desert Herald, wanda ya shiga tattaunawar ya shaida wa gidan talabijin na Channels cewa shida daga cikin waɗanda aka sako ‘yan gida ɗaya ne amma har yanzu hukumomin ‘yan sanda ba su tabbatar da faruwar lamarin ba.

Sai dai ba a bayyana ko an biya kuɗin fansa ga ‘yan ta’addar domin a sako su ba.

A cewar gidan talabijin na Channels, sunayen mutanen shida Abubakar Idris Garba, uban yara hudu; matarsa, Maryama Abubakar Bobbo, da babban ɗansu, Ibrahim Abubakar Garba mai shekaru 10.

Sauran sun haɗa da Fatima Abubakar Garba mai shekaru bakwai; Imran Abubakar Garba ɗan shekara biyar da Zainab Abubakar Garba mai shekara daya da rabi kacal.

Abubakar dai ɗa ne ga Chris Garba, tsohon shugaban mulkin soja na jihohin Kano da Benue.

Maharan sun kuma sako wata mata mai suna Aisha Hassan mai shekaru 60 da haihuwa, wacce ke fama da matsalar lafiya a lokacin da take tsare.

Idan ba a manta ba a ranar 28 ga watan Maris ne wasu ‘yan bindiga suka kai hari kan wani jirgin kasa da ke kan hanyarsa ta zuwa Kaduna daga Abuja, lamarin da ya yi sanadin mutuwar wasu fasinjoji yayin da aka yi garkuwa da wasu da dama.

Tun da farko dai ‘yan ta’addan sun buƙaci naira miliyan 100 kafin a sako waɗanda suka mutun kamar yadda wasu ‘yan uwa na waɗanda abin ya shafa suka bayyana.

A kwanakin baya ‘yan ta’addan sun sako wasu mutane biyar da fasinjojin suka yi garkuwa da su.

Waɗanda aka ceto sun hada da Farfesa Mustapha Umar Imam, wanda likita ne a asibitin koyarwa na Jami’ar Usman Dan Fodio da ke Sokoto, Akibu Lawal, Abubakar Ahmed Rufai Mukthar Shu’aibu da Sidi Aminu Sharif.

Ya zuwa yanzu, daga watan Yuni zuwa yau fasinjojin kasa da kasa 22 ne suka samu ‘yancinsu.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like