Connect with us

'Yansanda

Mahaifiyar matar da mijinta ya kashe akan biredi ta buƙaci adalci

Published

on

Cordelia Anene, mahaifiyar marigayiya Ogochukwu Anene, wadda ake zargin mijinta, Wilson Uwaechina, ya kashe ta a kan biredi, ta buƙaci a yi ma ‘yar ta adalci.

Marigayiyar, ‘yar asalin ƙauyen Umuokpu, Awka, jihar Anambra, ta auri Uwaechina, wanda ya fito daga jihar Enugu. Ana zargin ya kashe ta ne a wani rikici da suka yi a kan biredi.

KU KUMA KARANTA: Yadda wani mutum ya kashe matar sa saboda burodi

Cordelia ta buƙaci a yi mata adalci a lokacin da ta ziyarci kwamishiniyar mata da walwalar jama’a ta jihar Anambra, Ify Obinabo, a ofishinta a ranar Talata.

A yayin da take zargin mijin ne ya kashe ‘yarta, matar ta bayyana cewa marigayiyar Ogochukwu ta sha dukan tsiya daga mijin ne bayan ya cinye burodin data sayawa yara, kuma da yaran suka nuna suna son biredin sai mijin ya fusata harda tambayar dalilin da ya sa zasu tuhumeshi game da burodin. Ta ce hakan ne ya sa mijin ya riƙa dukan matar tasa da madubi da wasu abubuwa, wanda hakan ya sa ta fita hayyacinta.

Misis Anene ta bayyana cewa, kwanaki kaɗan bayan da ya yi mata dukan, an kwantar da ɗiyarta a asibitin Neja Foundation da ke Enugu, inda ta yi ta zubar da jini a ciki sakamakon raunukan da ta samu a lokacin da aka yi mata duka.

Ta ce, “Likitocin sun tabbatar da hakan ne bayan wani bincike da aka yi mata, inda suka tura mu asibitin koyarwa na jami’ar jihar Enugu da ke Ituku Ozalla.”

Ta koka da cewa yayin da duk waɗannan ke faruwa, ba a ga wanda ake zargin ba.

Mahaifiyar me rasuwar ta ce maimakon su nemi rahoton abinda ya kashe ta, ɗan sandan da ke kula da lamarin a Enugu ya roƙe su da su janye ƙarar.

Ta yi kira ga gwamnatin jihar Anambra da ta taimaka mata a yiwa ɗiyarta adalci.

Da yake mayar da martani, kwamishiniyar matar Obinabo, ta ce, “a halin yanzu ana ci gaba da bincike don gano ainihin musabbabin mutuwar marigayiya Ogochukwu Anene.”

Ta kuma buƙaci matan da ke cikin auratayya da su riƙa faɗa idan akwai matsala ta cin zarafi a aurensu, su kuma dinga neman taimako.

1 Comment

1 Comment

  1. Pingback: Yadda wani mutum shaƙe budurwarsa saboda cin amana, ya kuma cinna wa kansu wuta | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

'Yansanda

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

Published

on

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

Rundunar ’yan sandan Najeriya ta tube wa wasu jami’an ta biyar kaki sakamakon zargin su da karɓar cin hancin kuɗi kimanin Naira miliyan uku.

Mataimakin Shugaban ’yan Sanda mai kula da Shiyya ta shida ta da ke Jihar Kuros Riba, Jonathan Towuru, ya sanar a Kalaba cewa ’yan sandan sun kwace kuɗin ne da bakin bindiga a hannun wani mai abin hawa.

A makon jiya ne aka zargi jami’an da ƙwayar kuɗin da bakin bindiga a hannun wani mutum da rundunar ta sakaya sunansa.

Yanzu haka waɗanda ake zargin an tuɓe masu kaki amma ana tsare da su ana bincike, da zarar an same su da laifi kotu za a turasu ta yanke masu hukuncin da ya dace.

KU KUMA KARANTA: ’Yan sanda za su tantance ’yan banga a Yobe

Mataimakin shugaban ’yan sandan ya ce waɗanda ake zargin su da karɓar cin hancin kuɗi Naira milyan uku daga wannun wani.

Ko a kwanan baya irin haka ta taba faruwa a kan babbar hanyar Kalaba zuwa Ikom inda aka kama wasu ’yan sanda kan karbar na goro.

Tafiya a kan hanyar na yawan zargin ’yan sanda da kula da shingen bincike a kan hanyar da yawan tatsar su kuɗi.

Continue Reading

'Yansanda

‘Yan sanda sun kama mutum 2 da ake zargin sace mahaifiyar Rarara

Published

on

Yan sanda sun kama mutum 2 da ake zargin sace mahaifiyar Rarara

‘Yan sanda sun kama mutum 2 da ake zargin sace mahaifiyar Rarara

Rundunar ’yan sandan Jihar Katsina ta sanar da cafke wasu mutum biyu bisa zargin hannu a garkuwa da mahaifiyar fitaccen mawaƙin siyasar nan, Dauda Kahutu Rarara.

Mai magana da yawun rundunar a Katsina, ASP Abubakar Sadiq Aliyu ya ce “muna tsare da mutum biyu kan lamarin, muna ci gaba da bincike.”

Tun farko, Kwamishinan tsaro na Jihar Katsina, Nasiru Mu’azu ya ce an sace dattijuwar ce a daren Juma’a a ƙauyen Kahutu da ke Karamar Hukumar Ɗanja.

Mu’azu ya ce waɗanda suka sace matar sun yi hakan ta hanyar bi ta bayan gida, inda suka sace ta ba tare da jami’an da ke tsaron gidan sun sani ba.

Ya kuma bayyana cewa tuni aka tura jami’an tsaro waɗanda suka bazama cikin dazuka domin bin sawun ’yan bindigar.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan bindiga sun yi garkuwa da mahaifiyar mawaƙi Rarara

Neptune Prime Hausa ta ruwaito shaidu a kauyen sun ce da misalin karfe daya na dare ne dandazon ’yan bindiga suka kutsa gidan dattijuwar suka yi awon gaba da ita.

“A kafa suka zo, ba su yi harbi ba a lokacin da suka ka yi awon gaba da ita cikin ’yan mintoci.

“Dattijuwar ba ta bijire musu ba a lokacin da suka memi ta biyo su.

“Duk da cewa ’yan bindigar sun samu wasu mutane a gidan, amma mahaifiyar Rarara kaɗai suka ɗauka.

“Babu wani yunƙuri da aka yi na tunkarar ’yan bindigar a lokacin da suke tafiya da ita saboda bindigogin da suke ɗauke da su,” in ji wani mazaunin ƙauyen na Kahutu.
Ya ce, “Watakila maharan sun bar baburansu ne daga nesa suka tako zuwa cikin ƙauyen a kafa.

“Muna rokon Allah Ya kuɓutar da ita cikin koshin lafiya domin tana taimaka mana sosai a wannan ƙauyen.

“Danta Rarara mai yawan taimakon al’umma ne, kuma ya kawo mana abubuwan ci gaba sosai a garinmu,” in ji shi.

Continue Reading

'Yansanda

‘Yan sanda sun kama kawali na ’yan bindiga

Published

on

'Yan sanda sun kama kawali na ’yan bindiga

‘Yan sanda sun kama kawali na ’yan bindiga

Daga Muhammad Kukuri 

Wani wanda yake kai wa ’yan bindiga karuwai domin yin lalata da su ya shiga hannun jami’an tsaro.

’Yan sanda sun bayyana cewa kawalin ya kuma ƙware wajen yin safarar makamai ga ƙungiyar jagoran ’yan bindiga mai suna Arɗo, wanda ake nema ruwa a jallo a yankin Kagarko da ke Jihar Kaduna.

An kuma gano cewa mutumin wanda yake harkar hada-hadar tura kuɗi ta PoS, shi ke kai wa iyalan ’yan bindiga kuɗaɗe a yankin na Kagarko.

Dubun kawalin ta cika ne a yayin wani samamen haɗin gwiwa da ’yan sanda suka gudanar a yankin.

Kwamishinan ’Yan Sandan Birnin Tarayya, ya sanar ranar Talata cewa wanda ake zargin ya shaida musu cewa shi ke tsara yadda ake kai wa ’yan bindiga karuwai da miyagun ƙwayoyi da ma’aikatan lafiya a duk lokacin da suke buƙata.

KU KUMA KARANTA: Ƴan sanda a Kano sun kai mutanen da ake zargi da sayar da dala ba bisa ƙa’ida ba kotu

“Ya kuma amsa cewa yana yin dakon kuɗi tare da rabawa ga iyalan ’yan bindiga.

“A cewarsa, kuɗaɗen da ya raba wa iyalan ’yan bindiga sun haura Naira miliyan ashirin,” in ji kwamishinan ’yan sandan.

Igwe ya ce wanda ake zargin ya tabbatar musu cewa ’yan bindigar da ke ƙarƙashin Ardo sun kai 15 kowannensu da bindiga ƙirar AK-47.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like