Connect with us

Civil Defense

Kotu ta yanke wa wasu ‘yan Ghana masu safarar wiwi zuwa Najeriya, hukuncin ɗaurin shekaru 72 a gidan yari

Published

on

Hukumar hana sha da fataucin miyagun ƙwayoyi ta ƙasa (NDLEA) ta damƙe wasu ‘yan ƙasar Ghana 9 bisa laifin yunƙurin shigo da tabar wiwi kilogiram 10,843.95 zuwa Najeriya.

Mai shari’a Akintayo Aluko na babbar kotun tarayya da ke Legas a lokacin da yake yanke hukunci a kan lamarin, ya samu ‘yan Ghanan da laifin haɗa baki da kuma safarar tabar wiwi.

‘Yan Ghanan sun yi yunƙurin safarar tabar wiwi ta cikin teku inda aka yanke musu hukuncin ɗaurin shekaru 72 a gidan yari.

Rahotanni da dama sun nuna cewa tun da farko wasu jami’an hukumar tsaro ta Civil Defence ne suka kama su kuma aka tura su NDLEA domin ci gaba da bincike da gurfanar da su gaban kuliya.

Bayan binciken, an gano cewa an gurfanar da su gaban kotu mai lamba FHC/L/292C/2021. Waɗanda aka yanke wa hukuncin sun haɗa da; Victor Wuddah, Freeman Gazul, Adotete Joseph, Sottie Moses, Sottie Stephen, Christian Tette, Kanu Okonipa, Daniel Koyepti, and Kanu Natte.

1 Comment

1 Comment

  1. Pingback: An kama da hodar ibilis sakaye cikin abincin jarirai a Legas | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

'Yansanda

Asirin wani sojan gona ya tonu a jihar Kano

Published

on

Daga Shafaatu DAUDA, Kano

Rundunar hukumar kare rayuka da dukiyoyin Al umma ta jihar kano (civil defense) tayi nasarar kame Wani matashi Mai suna Umar A Alasan Mai shekara 31 a ƙaramar hukumar kumbotso.

Matsahin dai ansame shi da wayoyin salula, da kayan jamian tsaro na civil defense ɗauke da number aiki gamida ID card na hukumar.

Ƙunshin kayayyakin da aka samu a hannun wanda ake zargi da amfani da kayan rundunar tsaro ta civil defense dake kano

Jami in hulda da jama’a na hukumar ta civil defense ya tabbatar da faruwar lamarin, DSC ibrahim saminu Abdullahi, yace sun sami nasara ne tareda tallafin jami’an tsaro na ‘yansanda. Ya ƙara da cewa yazama wajibi suyi godiya da Al umma bisa yadda suke bawa wannan rundunar haɗin kai wajan Basu labarai na gaskiya.

Matsahin ya amsa lefinsa har ya roƙi da ayi masa afuwa. A nasa ɓangaren, mai magana da yawun hukumar yace dazarar sun kammala bincike zasu GURFANAR dashi a kotu don yimasa hukuncin da ya dace dashi.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like