Connect with us

Labarai

Kotu ta tsare wasu mutane 25 da ake zargi da laifin yin takardar jabu na KAROTA

Published

on

Wata kotun majistare da ke zamanta a Kano a ranar Talata ta bayar da umarnin a tsare wasu mutane 25 da ake zargi da damfara a gidan gyaran hali bisa samunsu da laifin yin takardun KAROTA na jabu.

Hukumar kula da zirga-zirgar ababen hawa ta jihar Kano, KAROTA, ta gurfanar da waɗanda ake tuhuma, waɗanda ba a bayar da adireshin gidansu ba, bisa zarginsu da laifin haɗa baki, da takardun jabu da kuma zamba.

Mai gabatar da ƙara, Tijjani Ibrahim, ya shaida wa kotun cewa waɗanda ake tuhumar sun aikata laifin ne a ranar 22 ga watan Yuli.

KU KUMA KARANTA: Kotu ta hana gwamnatin Kano rushe gine-gine a hanyar Jami’ar Bayero Kano

Ya yi zargin cewa a wannan ranar an kama wasu daga cikin waɗanda ake tuhuma a lokacin da suke da takardun jabun na KAROTA.

A cewar mai gabatar da ƙara, laifin ya ci karo da sashe na 97, 393 da 321 na kundin laifuffuka na jihar Kano.

Sai dai waɗanda ake tuhumar sun musanta aikata laifin.

Lauyan waɗanda ake ƙara, Nazifi Rabiu, ya buƙaci kotun da ta bayar da belin waɗanda ake ƙara kamar yadda sashe na 35 s (6), 36 (5) na kundin tsarin mulkin 1999 da aka yi wa kwaskwarima da sashe na 171 (3) na dokar shari’a ta jihar Kano 2019.

Sai dai babban alƙalin kotun, Halima Wali, ta bayar da umarnin a garƙame waɗanda ake ƙara a gidan gyaran hali, sannan ta ɗage ci gaba da shari’ar zuwa ranar 27 ga watan Yuli domin yanke hukunci kan buƙatar belinsu.

3 Comments

3 Comments

  1. Pingback: An kama wani tsohon soja a Bauchi bisa zarginsa da bai wa Boko Haram makamai | Neptune Prime Hausa

  2. Pingback: Masu aikata laifuka suna yin shigar matafiya don ƙwace motoci a Nasarawa | Neptune Prime Hausa

  3. Pingback: KAROTA a Kano sun kama jabun magungunan kashe ƙwari | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like