No menu items!

Sample Page Title

Date:

Kotu a Kano ta yanke wa matashin da ake zargi da cinnawa budurwarsa wuta ɗaurin shekaru 15

Daga Jameel Lawan Yakasai

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 1 ƙarƙashin jagorancin Mai shari’a Dije Abdu Aboki ta yanke wa wani matashi daga ƙaramar hukumar Takai hukuncin daurin shekaru 15 a gidan gyaran hali, bisa laifin yunkurin kisan kai ta hanyar cinnawa budurwarsa wuta.

An gurfanar da matashin mai suna Abdullahi Saidu, ɗan asalin garin Sakwaya da ke ƙaramar hukumar Takai, bisa zargin cinnawa budurwarsa Sa’adatu Ibrahim wuta saboda an dawo masa da kayan auren da ya kamata.

Kotun ta saurari shaidu uku daga masu gabatar da ƙara kuma lauyoyin gwamnati Barista Hajara Ado Sale da Barista Sadiya Sambo da kuma shaida ɗaya daga ɓangaren wanda ake ƙara.

KU KUMA KARANTA: Kotu a Kano ta tura Mutane 29 da ake zargi da Kashe DPOn Rano gidan Yari

Bayan nazarin shari’ar, kotu ta yanke masa hukuncin daurin shekaru 15, tare da umarnin ya biya diyyar Naira miliyan ɗaya ga wadda abin ya shafa, ko kuma ƙara shafe shekaru 5 a gidan yari idan ya kasa biyan kudin.

Bayan zaman kotu, Barista Hajara Ado Sale ta ce hukuncin ya dace da nauyin laifin, yayin da lauyoyin wanda aka yanke wa hukunci suka ƙi cewa komai ga manema labarai.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...