Connect with us

Kiwon Lafiya

‘Korona ta kashe sama da mutum dubu uku da ɗari biyar’

Published

on

Hukumar Lafiya ta Duniya ta ba da rahoton ɓullar cutar korona (COVID-19) guda 674,678 daga ranar 23 ga Janairu zuwa 25 ga Janairun 2023.

Bayanan da aka samu daga hukumar kiwon lafiya ta duniya wato WHO akan COVID-19 sun nuna cewa mutane 3,584 ne suka mutu sakamakon kamuwa da cutar a lokacin da ake nazari.

Wannan shi ne kamar yadda ƙungiyar lafiya ta duniya ta lura cewa, rigakafin COVID-19 ya kasance yana da matukar muhimmanci wajen kariya daga mummunan cuta da mutuwa, yayin da ƙwayar cutar ke ci gaba da yaɗuwa, kuma tana ci gaba da canzawa.

KU KUMA KARANTA:Ansamu masu cutar Ƙyandar-Biri a jihar Borno

Darakta Janar na hukumar ta WHO, Dr. Tedros Ghebreyesus, ya bayyana damuwarsa kan ƙaruwar adadin masu kamuwa da cutar COVID-19 a ƙasashe da dama.
Ghebreyesus ya ce Kwamitin gaggawa kan COVID-19 zai gana a wannan makon, don tattauna.

Rahoton da Majalisar Ɗinkin Duniya ta fitar ya nuna cewa,mutum 396,821 COVID-19 da aka tabbatar sun kamu da cutar a ranar 23 ga Janairu, tare da mutuwar 2,142. A ranar 24 ga Janairu, aƙalla 98,748 da aka tabbatar sun kamu da cutar tare da mutuwar 729.

Yayin da aka samu rahoton ɓullar cutar guda 179,108 da kuma mutuwar mutane 713 a ranar 25 ga watan Janairu.

Ya zuwa 25 Janairun 2023, an sami mutum 664,873,023 da aka tabbatar sun kamu da cutar COVID-19, gami da mutuwar mutum 6,724,248, kamar yadda hukumar ta WHO ta ruwaito.

A wani ci gaba mai alaka da wannan, ofishin WHO na Afirka a Brazzaville ya ce ‘yan Afirka na fitowa daga lokacin balaguro na sabuwar shekara ba tare da an samu ɓullar cutar ta COVID-19 a karon farko tun bayan barkewar cutar ba.

Duk da haka, ya ce raguwar sabbin lamuran da aka bayar na iya kasancewa wani ɓangare saboda ƙarancin gwajin COVID-19, amma abu mafi mahimmanci shi ne rashin lafiya mai tsanani, da kuma mace-mace, sun ragu sosai.

A Najeriya an sami ƙararraki ararraki a halin da ake ciki, Cibiyar Kula da Cututtuka ta Najeriya ta tabbatar da samun sabbin mutane 15 da suka kamu da COVID-19 a cikin kasar cikin mako guda. An sami sabbin kararraki 15 daga 14 ga Janairu zuwa 20, 2023.

Rahotanni sun nuna cewa an samu rahoton ɓullar cutar daga jihohi huɗu – Filato (8), Kano (3), Legas (3), da Kaduna (1). Sabbin kararrakin guda 15 sun kawo adadin waɗanda aka tabbatar sun kamu da cutar COVID-19 a kasar zuwa 266,507, a cewar NCDC.

Hukumar ta ce, “Ya zuwa yanzu an tabbatar da kamuwa da cutar guda 266,507, an sallami mutane 259,864 sannan an samu mutuwar mutane 3,155 a jihohi 36 da kuma babban birnin tarayya.

Tun da farko, Gwamnatin Tarayya ta ce duk matafiya na duniya da suka isa Najeriya a yanzu ana bukatar su bayar da shaidar rigakafin a wuraren da ake shigowa da su biyo bayan ɓullar cutar COVID-19 a kasashen China, Japan, Amurka da sauran kasashe.

Gwamnatin Tarayya ta kuma ce fasinjojin da ba su da alluran rigakafin da suka taho daga wasu ƙasashe na iya zama dole a yi musu allurar a filin jirgin.

A halin da ake ciki, Hukumar Kula da Lafiya a matakin farko ta ƙasa ta ce 65,679,094 na mutanen da suka cancanta da aka yi niyya don rigakafin COVID-19 a cikin ƙasar an yi musu cikakkiyar allurar rigakafin cutar yayin da 11,780,959 na mutanen da suka cancanta da aka yi niyya don rigakafin COVID-19 an yi musu wani ɓangare na allurar tun daga ranar 20 ga Janairu, 23.

A duniya baki ɗaya, an yi allurar rigakafin cutar guda 13,156,047,747 tun daga ranar 24 ga Janairun 2023.

1 Comment

1 Comment

  1. Pingback: Mutum 202 sun mutu sakamakon kamuwa da cutar COVID-19 a Oyo – NCDC | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Kiwon Lafiya

Gwamnatin tarayya ta hana amfani da sirinjin allura na ƙasashen waje a manyan asibitoci ƙasar

Published

on

Gwamnatin tarayya ta umurci dukkan shugabannin manyan asibitocin gwamnatin tarayya da su sayi allura da su riƙa amfani da allura da da ake ƙera su a gida kuma hukumar NAFDAC ta amince da su.

Sabuwar umarnin na ƙunshe ne a cikin wata takardar ga dukkan shugabannin asibitoci mai ɗauke da sa hannun ƙaramin ministan lafiya, Dakta Tunji Alausa, a yau Juma’a.

Ministan ya ce an ba da wannan umarnin ne domin bunƙasa samar da kayayyakin da ake ƙera wa a cikin gida da kuma kare masana’antun ƙasar daga kwararar kayayyakin ƙasashen waje.

Sanarwar ta kuma umarci hukumar ta NAFDAC ta dakatar da bayar da lasisin shigo da allura da sirinji da aka ƙera daga ƙasashen waje.

Alausa ya ce ɓangaren lafiya ya gano masana’antar har haɗa magunguna ta cikin gida da ke samar da allura da sirinji waɗanda ke cikin matsala matuƙa saboda wannan mummunar harkar.

Ya kuma ce daga cikin kamfanonin har haɗa magunguna guda tara na cikin gida da suke samar da allura da sirinji shekaru takwas da suka gabata, shida sun rufe saboda zubar da kayayyakin da ba su da inganci a kasuwa.

KU KUMA KARANTA:NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

“Shugaban ƙasa ya ba da umarnin cewa dole ne a daina wannan. Dukkanmu mun amince da ɗaukar matakan da suka dace don magance wannan mummunan yanayi cikin gaggawa.

“A bisa haka, hukumar ta NAFDAC ta dakatar da bayar da lasisin shigo da allura da sirinji da aka ƙera daga ƙasashen waje.

“Haka kuma shi ne a soke jerin sunayen kamfanonin da ke da hannu wajen shigo da waɗannan kayayyakin da ke ci gaba,” in ji shi

Continue Reading

Kiwon Lafiya

Amfanin ‘Dental floss’ a haƙora don tsaftace baki

Published

on

Daga Aisha Musa Auyo

Dental floss dai wani zare ne siriri na roba da ake sawa a tsakanin haƙora don cire abincin da ya maƙale a wurin. Wannan abinci da ke maƙale a tsakanin haƙora, brush ba ya fitar da shi. Shi ne yake taruwa ya zama ‘plaque’. Shi plaque ɗin wannan abincin da ya maƙale ne yake taruwa sai ya zama abincin bacteria.

Wannan dattin yana sa baki wari, yana sa haƙora su canza kala. Yana sa haƙora su yi ta ciwo wataran ma har sai an cire haƙorin, domin wannan bacteriar da ke ci daga gareshi tana kashe haƙori.

To shi wannan zaren yana zuwa a nau’i daban-daban, an yi shi ne siriri yadda ze iya shiga tsakanin haƙora yana fito da duk abin da ya maƙale ba tare da an wahala ba ko an ji zafi. Wani yakan zo da ƙamshin minti, vanilla, da sauransu, wani kuma kawai zaren ne babu ƙamshi.

Mafi yawancin ciwon haƙori ko warin baki wannan maƙallen abincin ke kawo shi. Idan mutum ya je Asibitin haƙori, akan yi masa wannan sakace tsakanin duk haƙoransa duka. Wato duk ranar da kuka fara flossing zai sha mamakin abin da zai fito tsakanin haƙoranku.

KU KUMA KARANTA: Sama da mutane miliyan 73 ne ke fama cutar ruɓewar haƙora a Filipin

Wato abin ya bani mamaki da na tambayi mutane ko suna flossing na ga da yawansu ba su ma san mene ne shi ba. Kamata ya yi flossing ya zama normal kamar brush. A ƙa’ida akan so mutum ya yi wannan sakacen tsakanin haƙoran kamar sau biyu a rana, yadda yake brush, amma mutum zai iya yin fiye da haka. In da hali duk lokacin da mutum ya ci abinci ya kamata ya yi flossing.

Akwai mouth wash da kan taimaka wajen fitar da waɗannan maƙallalun abincin, yayin da aka kurkure baki da shi na mintuna. Haka zalika, kurkure baki da ruwan kananfari ma na taimakawa wajen fiddasu. Amma babu abin da ya kai saka wannan zare a tsakanin haƙora ɗaya bayan ɗaya fitar da wannan abu da ke maƙalewa a tsakanin haƙoran.

Dan Allah a guji tsinken sakace, ba ɗaya yake da floss ba. Shi tsinken yana da kauri yana sa a samu rami tsakanin haƙoran da ake yawan sakace wa. Sannan katako ne yakan karye ma, kuma yakan jima mutum rauni.

A taƙaice, yin floss na ƙara wa mutum lafiyar haƙora, kyan haƙora, numfashi mai tsafta, da kuma jin daɗi wajen mua’amala da jamaa. Yin floss na raba mutum da ciwon haƙori, da kuma dauɗar haƙora. Floss na da sauƙin kuɗi sosai, ana iya samunsa a manyan shaguna, ko asbitin haƙori, har ma da wurin masu sayar da robobin abincin biki, domin ana sa shi a cikin packs ɗin abinci.

Dan Allah ka da mu yi wasa da yin floss. Akwai Hadisin da Annabi Muhammad (SAW) ya ce, ba dan ka da ya takurawa al’ummarsa ba, da ya mayar da yin aswaki kafin yin kowacce sallah ya zama wajibi. Wannan yana nuna mana tsantsar amfanin tsaftar baki ko a addini ma.

Continue Reading

Kiwon Lafiya

Cutar sanƙarau ta kashe mutum 85 a Yobe

Published

on

Daga Ibraheem El-Tafseer

Gwamnatin jihar Yobe ta ce cutar sanƙarau ta kashe mutum 85 tsakanin Janairu da Afrilu sakamakon ɓarkewar cutar a jihar.

Kwamishinan lafiya na jihar, Dakta Muhammad Lawan Gana ne ya tabbatar da hakan a wani taron manema labarai a birnin Damaturu.

Ya ƙaryata rahotannin da ake yaɗawa a shafukan sada zumunta da ke cewa cutar ta yi ajalin sama da yara 200 cikin mako biyu inda ya ce haƙiƙanin adadin shi ne 85.

Ya kuma ce fiye da marasa lafiya 2,510 da suka kamu da cutar a jihar sun samu sauƙi kuma an sallame su daga asibiti.

KU KUMA KARANTA: Gwamnati ta musanta mutuwar mutum 200 sanadiyar baƙuwar cuta a Yobe

Dakta Gana ya kuma ce an tura jami’an lafiya na sa kai sama da 200 zuwa sassan ƙananan hukumomin Potiskum da Fika a wani ɓangare na ƙoƙarin da ma’aikatar take na daƙile cutar.

Ya ce ma’aikatan lafiya sun bi gida-gida domin ganowa tare da tura mutanen da ke da cutar asibiti.

Yankunan arewacin Najeriya na fama da matsanancin zafi a tsukin nan, yanayin da ke haddasa cutar ta sanƙarau.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like