Connect with us

Kannywood

Jarumin Kannywood, Karkuzu ya makance, yana kukan neman taimako

Published

on

Fitaccen jarumin Kannywood, Abdullahi Shuaibu wanda aka fi sani da Karkuzu ya makance kuma yana fama da rashin lafiya.

Jarumin, wanda aka yaɗa bidiyonsa a shafukan sada zumunta, ya nemi taimakon kuɗi, inda ya bayyana cewa ya yi rashin lafiya tun watan Disambar 2020.

Shuaibu ya fara fitowa a masana’antar nishaɗantarwa ta Hausa a shekarun 1980 tare da shahararriyar wasan kwaikwayo mai suna Karkuzu na Bodara wanda ya sanya ake masa laƙabi da Karkuzu.

A zantawarsa da wannan jarida bayan faifan bidiyo, Karkuzu ya ce, “Yanzu na makance kamar yadda nake magana da ku. Ina matuƙar buƙatar taimakon kuɗi. Ba ni da abincin da zan ci da ciyar da iyalina.

KU KUMA KARANTA: Yadda mutuwar Alhaji Mala na shirin ‘Daɗin Kowa’ ta jijjiga Kannywood

“Gidan da nake zaune yanzu za a sayar. Idan sun sayar da wannan gidan, ban san inda zan dosa ba. Don haka ne nake neman taimako daga ‘yan Najeriya da su kawo min agaji.

A ƙalla ‘yan Najeriya su taimaka min sayan wannan gidan da nake zaune.”

Dangane da makanta, ya ce, “An min aiki sau biyu, amma a ƙarshe likitoci sun ce glaucoma ce, kuma ba zan sake gani ba. Na yarda da hakan a matsayin makoma ta. Amma ya kamata ‘yan Nijeriya su taimake ni. Kawo min gidan nan, da abinci.”

Masana’antar Kannywood na da ƙungiyoyi da dama, amma akwai zargin cewa ‘yan wasan kwaikwayo da dama ba sa kula da su idan ba su da lafiya kuma suna buƙatar taimako.

Zuwa haɗa wannan rahoto, ɗan wasan ƙwallon ƙafa na Najeriya Ahmad Musa ya ba shi kyautar naira dubu ɗari biyar, sannan ya ce a nemo gida na naira miliyan biyar zai saya masa.

1 Comment

1 Comment

  1. Pingback: Ɗan | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Kannywood

Kannywood ta ba wa Hisbah tabbacin goyon baya a Kano

Published

on

Bayan ce-ce-ku-ce, Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta sake zama da daraktoci da furdusoshi da jarumai da sauran masu ruwa da tsaki a Kannywood don tsaftace harkar fim da nufin kau da ayyukan baɗala a jihar.

A jawabansu daban-daban, Shugaban Ƙungiyar MOPPAN ta Ƙasa Dokta Ahmad Sarari da takwaransa na Jihar Kano Ado Ahmad Gidan Dabino da Shugaban Ƙungiyar Jarumai Alasan Kwalle sun nuna jin daɗinsu game da taron inda suka sha alwashin ba wa Hisbah goyon baya tare da alkawarin cewa nan gaba za a samu gyara a harkar fim ɗin.

Wannan shi ya kawo ƙarshen ce-ce ku-cen da aka yi ta yi game da ganawar Hukumar da ’yan fim na farko, wanda mafi yawansu suka ƙaurace wa bisa hujjar cewa Hisbar ba ta bi hanyar da ta dace wajen gayyatar su ba.

KU KUMA KARANTA: ’Yan Kannywood da dama sun ƙaurace wa taron da Hisbah ta gayyata a Kano

Hukumar ta sake miƙa musu goron gayyata a karo na biyu wanda suka amsa a ƙarƙashin jagorancin ɗan gidansu wato Shugaban Hukumar Tace Finafinai da Dab’i ta Jihar Kano Abba Almustapha.

Kwamanda-Janar na Hukumar Hisbah Shaikh Aminu Ibrahim Daurawa ya bayyana cewa ƙorafe-ƙorafe da suke yawan samu daga Kanawa da sauran sassan Najeriya kan yadda ’yan fim ke nuna abubuwan da suka saɓa wa addinin Musulunci da al’adun Hausawa a cikin finafinansu ya sa suka ga dacewar zama da masu ruwa da tsaki a harkar fim don laluɓo hanyoyin kawo gyara a cikin harkar.

“Ita Hukumar Hisbah an kafa ta ne don ta saita al’umma a kan koyarwar addinin tare da yi musu katanga daga aikata munanan ayyuka.

“Muna so a laluɓo hanyoyin da za a rage nuna abubuwa da suke na tir tare da ci gaba da nuna abubuwa da za su dabbaka addinin da kyawawan koyarwar al’adun Hausawa a harkar fim,” in ji Daurawa.

A nasa ɓangaren, Abba Almustapha ya bayyana cewa tuni ’yan fim din suka amince za su zama masu bin doka.

Abba Almustapha ya jaddada cewa nan ba da dadewa ba hukumomin biyu za su shirya taron ƙara wa juna sani da ’yayan Kannywood don ilimintar da su kan abin da ya shafi fim ta fuskar addinin Musulunci inda za a gayyato fitattun malaman Musulunci don tattauna tare da laluɓo hanyoyin da za a kai harkar fim ɗin ga tudun mun tsira.

Continue Reading

Kannywood

Ɗan wasan ƙwallon ƙafa Ahmed Musa, ya cika alƙawari, ya sayawa Karkuzu gida

Published

on

Kamar yadda Neptune Hausa ta kawo labarin cewa shahararren ɗan wasan Nijeriya Ahmed Musa MON ya yi alƙawarin sayawa Baba Karkuzu gida a yau Talata, alƙawari ya cika.
Alhamdulillah an sayi gida an kuma karɓi takardun gidan.

Kamar yadda kuke gani a hoto Baba Karkuzu ne riƙe da Jessy ɗin Ahmad Musa tare da takardan gidan shi cikin farin ciki da godiyar Allah (T).

Jarumin Kannywood, Karkuzu ya makance, yana kukan neman taimako

Ga waɗanda suka taimaka, Baba yace a isar masa da godiya a gare su, Ubangiji Allah ya sakawa kowa da alkhairi, Allah ya biyawa kowa buƙatar shi, wanda suka taimaka kuɗi da wanda suka taimaka da addu’a.

Dukkan mu Allah ya sakawa kowa da gidan Aljannah, Allah ya dube mu lokacin da muke cikin tsanani, Allah ya suturta mu da suturar shi mara yankewa, Allah ya rufa mana asirin mu. Ameen ya Allah.

Continue Reading

Kannywood

Da gaske ne auren jaruma Wasila Isma’il da Al-Amin Ciroma ya mutu?

Published

on

Auren nan mai ban sha’awa na tsohuwar jarumar Kannywood, Wasila Isma’il, da darakta kuma jarumi Al-Amin Ciroma, ya mutu, kamar yadda mujallar Fim ta wallafa a yau.

Tun a kwanan baya mu ke jin ana ta raɗe-raɗin mutuwar auren, amma sai mu ka ɗauka irin ji-ta-ji-tar nan ce da aka saba yaɗawa game da ‘yan fim.

Amma a yanzu mujallar Fim ta tabbatar da mutuwar auren bayan wakilan mu sun tattauna da makusantan ma’auratan waɗanda suka tabbatar mana da sahihancin labarin.

Tsegumi a kan rubuwar auren dai ya faro ne daga yadda wasu suka gano Hajiya Wasila ta cire kalmar ‘Misis Ciroma’ daga sunan ta kamar yadda ta saba yi a duk wani rubutu da za ta yi, sai aka ga ta mayar da sunan ta ‘Wasila Isma’il’ kawai. Mutane sun yi ta neman dalilin hakan.

KU KUMA KARANTA: Yadda mutuwar Alhaji Mala na shirin ‘Daɗin Kowa’ ta jijjiga Kannywood

Majiya ƙwaƙƙwara ta tabbatar wa da mujallar Fim cewa mutuwar auren ya faru ne kimanin watanni biyu da suka gabata. “A yanzu ko dai ta kammala idda ko dai ta na gab da kammalawa,” inji wani bakin da ba ya ƙarya.

Majiyar tamu ta ce wani abu kuma wanda ya saɓa a iya gane mutuwar auren farat ɗaya ba shi ne saboda bisa al’adar mu da zarar aure ya mutu sai a ga mace ta kwashe kayan ta daga gidan miji, to amma ita Wasila tun da su ka rabu a gidan auren ta ke zaune tare da ‘ya’yan ta, ba ta tashi ba.

Masu ba mu labarin ba su bayyana takamaiman dalilin mutuwar auren ba.

Wakilan mu sun tuntuɓi Wasila da Malam Al-Amin kan wannan al’amari maras daɗi da ya faru a tsakanin su, to amma ba wanda ya yarda ya yi bayani.

Auren Wasila da Al-Amin ya na ɗaya daga cikin aurarrakin ‘yan Kannywood da ake kafa misali da su na zaman da ya daɗe sosai, har da ƙaruwar ‘ya’ya. ‘Ya’ya biyar Wasila ta haifa masa, mata uku, maza biyu, amma ɗaya ya rasu.

Idan kun tuna, a ranar Alhamis, 6 ga Oktoba, 2022 Al-Amin Ciroma da Wasila sun yi bikin cikar su shekara 20 da aure, wanda hakan ya jawo masu addu’ar fatan alheri da roƙon Allah ya ƙaro shekaru masu yawa nan gaba.

Tun wajen ƙarfe 10:00 na safe a ranar, daraktan ya wallafa wata fosta mai ɗauke da hoton sa da iyalin sa gaba ɗaya a soshiyal midiya, kuma ya yi wani rubutu kamar haka: “Our 20th Wedding Anniversary,” sannan ya wannan lissafin: “Watanni 240, makwanni 1,043, kwanaki 1, 306, sa’o’i 176, 344, mintuna 10, 520, 640, saƙwanni 631, 238, 400, ‘ya’ya biyar, ɗaya ya rasu, Allah ya jiƙan Muhammad Al-Baƙir, amin.”

Haka kuma a dai wannan ranar, mujallar Fim ta buga hirar musamman da ta yi da Ciroma ɗin, inda ya bayyana sirrin ɗorewar auren nasu.

Ya ce, “Alhamdulillah. Shekara ashirin a zaman aure ana tare, sai dai hamdala. Ka san rayuwar aure rayuwar addini ce, kamar yadda kowa ya sani. Tilas ne mutum ya jajirce, ya kuma yi haƙuri da duk jarabawan da zai ci karo da su na zaman taren, musamman a yanzu ma da riƙon auren ya ke da tsada a ƙasar Hausa. Galibi, za ka iske da dama cikin aurarrakin yanzu suna saurin rugujewa saboda matsaloli daban-daban na haɗakar zamantakewa.

“To, ka ga kenan, duk wanda Allah ya raya shi har ya shafe shekaru irin wannan ana tare, shakka babu, tilas ka yi godiya a gare shi.”

Ciroma, wanda shi ne kuma kakakin Haɗaɗɗiyar Ƙungiyar masu shirya Fina-finai ta Nijeriya (MOPPAN), ya yi tsokaci kan masu ‘yan fim ba su daɗewa a aure, ya ce, “Auren ‘yan fim shi ma wata makaranta ce ta daban. Baya ga sa ido da mutanen gari ke yi mana, akwai yadda kuma ake kallon mu. Ana saurin nuna cewa matan fim ba sa zama a gidajen su na aure. Hakan ne ma ya sa ake yi masu kuɗin goron.

“Amma kuma da hikimar Allah, sai mu mu ka tsallake duk waɗannan maganganun.”

Ya bayyana wani abu wanda ba kowa ya sani ba, ya ce: “Ba na tsammanin akwai wata ‘yar fim da su ka yi aure tare da Wasila wadda ta kai ta daɗewa ba tare da wani rikici ko ce-ce-ku-ce ba.

“Don haka na ke yin ƙira ga sauran ‘yan’uwa da abokan arziƙi a cikin masana’antar Kannywood da mu ci gaba da ba maraɗa kunya, mu jajirce mu riƙe wa juna amana.”

Abin ikon Allah, sai ga shi su ma sun faɗa cikin wannan rami da wasu suka faɗa.

Shakka babu, wannan mutuwar auren za ta ba mutane mamaki matuƙa, kamar irin mutuwar auren jaruma Mansurah Isah da jarumi kuma mawaƙi Sani Musa Danja da mujallar Fim ta fara bayyana faruwar sa a ranar 27 ga Mayu, 2021.

Sai dai kamar yadda wani daga cikin su ya faɗa wa mujallar Fim, “Allah ya sa hakan shi ya fi alheri.”

Idan da rabon komawa kuma, mu na addu’ar Allah ya sasanta tsakanin su, amin.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like