Connect with us

Ɗalibai

Jami’ar Jihar Yobe ta yi bikin zuwan sabbin ɗalibai 2,740

Published

on

Mataimakin Shugaban Jami’ar Jihar Yobe dake Damaturu, Farfesa Mala Mohammed Daura, ya bayyana cewa Jami’ar ta kai wani mataki na ɓullo da shirin koyon aikin jinya a Jami’ar, wato ‘B.Sc Nursing’ a Kwalejin Kimiyyar Kiwon Lafiyar.

Mataimakin shugaban jami’ar ya bayyana hakan ne a yau Laraba 19 ga watan Afrilu 2023 a wajen bikin maraba da zuwan sabbin ɗaliban jami’ar karo na 14.

Farfesa Daura ya kuma bayyana cewa Jami’ar na duba yiwuwar ɓullo da wasu shirye-shirye na ilimi a Kwalejin Kimiyyar Likita kamar Dentistry, Medical Laboratory Science da Radiography.

KU KUMA KARANTA: An yi kira ga hukumar Lantarki ta YEDC ta inganta yadda take ba da wuta a Yobe

Ya ce Jami’ar ya zuwa yanzu tana da ɓangaren Kwalejin Kimiyyar Kiwon Lafiyar Jama’a, rassa biyar, sassan ilimi 31 da ke gudanar da shirye-shiryen ilimi 48, da cibiyoyi na musamman guda 6.

Mataimakin shugaban jami’ar ya ƙara da cewa sabon ɓangaren noma da aka kafa tare da sassa huɗu na ilimi a yanzu haka ta fara karatu da ɗalibai 149 a matakin farko.

Ya ce jami’ar na samun ci gaba cikin sauri ta fuskar shirye-shiryen ilimi da kuma shigar da ɗalibai, inda ya jaddada cewa jimillar ɗaliban sun kai 11,022 kuma sun haɗa da sabbin ɗalibai 2,740 da kuma ɗalibai 8,282 da suka dawo daga matakin farko.

Farfesa Daura ya ci gaba da bayyana cewa ɗaliban da suka samu gurbin karatu na shekarar 2022/2023 su ne waɗanda suka nemi gurbin shiga ta hanyar UTME da DE a lokacin gudanar da jarabawar JAMB na 2021 da 2022.

Ya kuma buƙaci sabbin ɗaliban makarantar da su riƙa tunawa da irin rantsuwar da suka sanyawa hannu wajen gudanar da ayyukansu a ciki da wajen Jami’ar.

Mataimakin shugaban jami’ar ya kuma shawarci ɗaliban da su guji duk wata munanan ɗabi’u kuma su fuskanci karatunsu, su shiga ayyukan karatu tare da zama jakadu nagari na wannan Jami’a.

Daga nan sai Farfesa Daura ya ja hankalin iyaye da su yaba da ƙoƙarin gwamnatin jihar Yobe da gwamnatin tarayya wajen samar da ababen more rayuwa na koyo da koyarwa.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Ɗalibai

Sai da aka kashe na’urorin ɗaukar hoto kafin a sace ɗaliban Kogi – Gwamna Ododo

Published

on

Rahotanni daga jihar Kogin Najeriya na cewa an kashe duka na’urorin ɗaukan hoto a jami’ar kimiyya da fasaha ta Confluence University da ke jihar kafin a sace wasu ɗaliban makarantar a cewar Gwamna Usman Ododo.

A ranar Alhamis wasu ‘yan bindiga suka kutsa jami’ar wacce ke Osara suka sace ɗalibai tara cikin dare.

Ya zuwa lokacin haɗa wannan rahoto ba a ji ɗuriyar ɗaliban ko waɗanda suka sace su ba.

Ododo ya bayyana hakan ne yayin da ya kai ziyarar ganewa idonsa jami’ar a ranar Asabar.

“Binciken da muka gudanar ya zuwa yanzu, ya nuna cewa, duka na’urorin da muka saka an kashe su, kuma wannan ba wani abu ba ne illa zagon ƙasa daga mutanen cikin gida.” Ododo ya ce.

Gwamna Ododo ya yi ƙira ga iyayen ɗaliban da su kwantar da hankulansu saboda jami’an tsaro suna bin diddigin al’amarin yana mai cewa buƙatar gwamnati a yanzu shi ne a ceto ɗaliban.

KU KUMA KARANTA:Muna ƙoƙarin kuɓutar da ɗaliban jami’ar da ‘yan bindiga suka sace – Gwamnatin Kogi

Batun satar ɗalibai a makarantun firaimare da sakandare da ma jami’o’i a Najeriya ba baƙon abu ba ne musamman a arewaci.

‘Yan bindiga kan sace ɗalibai da dama su kutsa da su cikin daji har sai an biya kuɗin fansa kafin a sako su.

Satar mutane domin neman kuɗin fansa, babbar matsala ce a mafi akasarin jihohin arewa maso yammacin Najeriya.

Hukumomin ƙasar sun ce suna iya bakin ƙoƙarin su wajen ganin sun kawo ƙarshen wannan al’amari.

Continue Reading

Ɗalibai

Za’a a fara koyar da harsunan Ijaw, Faransanci, da Sinanci a makarantun a jihar Bayelsa

Published

on

Daga Maryam Umar Abdullahi

Gwamnatin Bayelsa ta ce za ta ba da fifiko kan koyo da koyar da harsunan Ijaw, da Faransanci, da kuma Sinanci a makarantun gwamnati a jihar.
Mataimakin gwamnan jihar, Mr. Lawrence Ewhrudjakpo ya bayyana a cikin wata sanarwa da babban mai taimaka masa na musamman kan harkokin yaɗa labarai, Doubara Atasi, ya fitar a jiya Alhamis cewa, ƙaruwar tasirin tattalin arziƙin ƙasar China a harkokin duniya a matsayinta na babbar jigo a harkokin cinikayya da cinikayyar duniya, ya nuna kamatar tabbatar da shigar da ƙarshen ƙasar China a cikin manhajar karatu.

KU KUMA KARANTA: Firaiministan Nijar, Lamine Zeine, ya caccaki ECOWAS  kan yin zagon ƙasa

Ewhrudjakpo ya bayyana cewa, gwamnati za ta fi maida hankali kan harsunan ne domin, baya ga muhimman darussa na kimiyya, harsunan za su taimaka wajen samar da yaran da za su ci gajiyar damar sana’ar da waɗannan darussa ke bayarwa a nan gaba.

Ana magana da harshen Ijaw ne a yankin Niger-Delta da ya ƙunshi jihohin Delta, Bayelsa da kuma Cross Rivers. Akwai kuma waɗannan suke harshen da ake ƙira “Arogbo-Ijaw” a jihar Ondo.

A shekarun nan, masana na jadada buƙatar ganin gwamnatoci sun ɗauki matakan raya al’adu da harsuna da ake gani aka kara watsi da su sabili da ci gaba na zamani.

Continue Reading

Ɗalibai

A bawa ɗalibai tallafin karatu, ba bashin kuɗin karatu ba – ƙiran ASUU ga gwamnatin tarayya

Published

on

Ƙungiyar malaman jami’o’i ta Najeriya (ASUU) ta buƙaci Shugaba Bola Tinubu ya sauya dokar ba da bashin karatu ga ɗalibai da ya amince da ita, zuwa tallafin karatu domin bai wa ɗalibai masu ƙaramin ƙarfi damar samun ilimi mai zurfi.

A wata hira da gidan Talbijin na Channels ranar Lahadi, shugaban ASUU ya ce bashin karatun ba abu ne mai yiwu ba. A cewarsa, bayar da bashi don yin karatu “ba zai ɗore ba”.

Farfesa Emmanuel Osodeke ya ce, “tunanin bayar da bashin karatu ga ɗalibai ya zo ne a 1972 kuma yana cikin harkokin bankuna da aka kafa”.

KU KUMA KARANTA: NURTW ta goyi bayan shugaba Tinubu kan cire tallafin man fetur

Ya yi iƙirarin cewa mutanen da suka karɓi bashin, ba su taɓa biya ba, kuna iya zuwa ku bincika. A shekarar 1994 ko 1993, sojoji sun kafa dokar soja mai lamba inda suka kafa hukumar bayar da bashi ga ɗalibai. Sai Majalisar dokoki ta daidaita ta a shekara ta 2004 kuma a cikin shekara ɗaya, ta wargaje. Kuɗaɗen suka ɓace. Muna so mu ga yadda wannan zai bambanta”.

A cewarsa, akwai ɗalibai sama da miliyan ɗaya a jami’o’in gwamnatin Najeriya kuma rancen ba zai iya biyan kuɗin karatun ɗalibai ba.

A ranar Litinin ne Shugaba Tinubu ya sa hannu a kan dokar ba da bashi ga ɗalibai domin cika alƙawarin da ya ɗauka a lokacin yaƙin neman zaɓensa.

Shugaban majalisar wakilai ta 9, Femi Gbajabiamila, wanda yanzu shi ne shugaban ma’aikatan fadar shugaban ƙasa ne ya ɗauki nauyin gabatar da ƙudurin dokar a majalisa.

Dokar ta tanadi ba da bashi maras ruwa ga ɗalibai masu ƙaramin ƙarfi a Najeriya.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like