Connect with us

Kasashen Waje

Iran ta ce a shirye take ta taimakawa jamhuriyar Nijar, don shawo kan takunkuman da aka ƙaƙaba mata

Published

on

Daga Maryam Umar Abdullahi

Iran ta faɗa a jiya Laraba cewa, a shirye take ta taimaka wa Jamhuriyar Nijar da aka yi juyin mulki, don shawo kan takunkumin da ƙasashen duniya suka ƙaƙaba mata, a daidai lokacin da Iran ke ƙoƙarin rage maida ita saniyar ware da aka yi, ta hanyar ƙarfafa alaƙa da ƙasashen Afirka.

Mataimakin shugaban ƙasar Iran, Mohammad Mokhber, ya ce ƙasarsa ta yi Allah wadai da takunkumin na rashin Imani, a wata ganawa da Firai Ministan Nijar Ali Mahaman Lamine Zeine.

Ya ƙara da cewa “Babu shakka zamu bayyanawa abokanmu daga Nijar abinda mu ka koya a wannan”

Tun bayan nasarar juyin Musulunci a shekarar 1979 aka ƙaƙaba wa Iran takunkumi mai tsanani daga ƙasashen duniya, amma ta samu hanyoyin kaucewa wasu daga cikinsu.

An ƙaƙaba wa Iran takunkuman ƙasa da ƙasa masu tsauri tun bayan juyin-juya hali na Musulunci a shekara ta 1979, amma ta samu hanyoyi fidda kanta daga waɗansu.

KU KUMA KARANTA:Sama da mutane 70 ne suka mutu, sakamakon rugujewar mahaƙar Zinari a ƙasar Mali

Har ila yau Iran na fuskantar matsin takunkuman da Amurka ta ƙaƙaba mata tun bayan ficewar da Washington ta yi a shekarar 2018 daga wata muhimmiyar yarjejeniyar nukiliya da ta bai wa Iran sassaucin takunkumi domin daƙile ayyukanta na nukiliya.

Ƙasar Nijar na fuskantar tsauraran takunkumin tattalin arziƙi da na kuɗi daga ƙungiyar ƙasashen yammacin Afirka bayan juyin mulkin da sojoji suka yi a watan Yulin 2023 wanda ya hamɓarar da zaɓaɓɓen shugaban ƙasar Mohamed Bazoum.

A cikin taron, Mokhber ya yaba da “nasarar” da ƙasar da Faransa ta yi wa mulkin mallaka ta yi, na “kafa gwamnati mai cin gashin kanta” a lokacin wannan juyin mulkin.

Ƙasashen biyu sun tattaɓa hannu kan yarjeniyoyi da dama a fannoni daban-daban da suka haɗa da makamashi, kiwon lafiya da kuɗi.

A watannin baya-bayan nan Iran ta tabbatar da goyon bayanta ga shugabannin da suka ƙwace mulki ta hanyar juyin mulki a Mali, Burkina Faso da Nijar.

Shugaban ƙasar Iran Ebrahim Raisi a watan Satumba ya yaba da “jajircewar waɗannan ƙasashen na Afirka” waɗanda ke fuskantar “manufofin Turai da mulkin mallaka.”

Iran, kamar Rasha da Turkiyya, a shirye take ta ƙarfafa tasirinta a nahiyar Afirka, inda take ƙarfafa alaƙa a ƙoƙarin ta na rage wariyar launin fata da maida ta saniyar ware da aka yi, da kuma kawar da tasirin takunkumin.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Kasashen Waje

COPA America: Panama ta yi nasara kan Amurka

Published

on

COPA America: Panama ta yi nasara kan Amurka

COPA America: Panama ta yi nasara kan Amurka

Hukumar ƙwallon ƙafa ta Amurka ta yi Allah wadai da kalaman nuna wariyar launin fata ga ‘yan wasanta a ranar Alhamis, bayan da Panama ta yi nasara a kan Amurka da ci 2-1 a gasar cin kofin Copa America.

A wani saƙo da ta wallafa a shafin X, hukumar ƙwallon ƙafa ta Amurka ta ce “Babu shakka, babu wuri a cikin wasa na irin wannan halayya ta nuna ƙiyayya da wariya.”

Sanarwar ta ƙara da cewa “Waɗannan ayyukan ba kawai ba za’a amince da su ba ne, amma kuma sun saɓa wa kimar mutuntawa da haɗa kai da muka ɗauka a matsayin hukuma.”

KU KUMA KARANTA:Manchester City ta lashe Firimiyar Ingila sau huɗu a jere

Timothy Weah, wanda baƙar fata ne, yana ɗaya daga cikin ‘yan wasan da aka ci zarafin su. An bai wa ɗan wasan gaba na Amurka jan kati kai tsaye a minti na 18 da fara wasa, saboda hannu da ya sa ya bugi ɗan wasan Panama a bayan kan sa a lokacin da ƙwallon ta fita wajen filin wasa.

Ɗan wasan Amurka Folarin Balogun ya zura ƙwallo a minti na 22 da fara wasan bayan an bai wa Weah jan kati kafin ɗan wasan Panama Blackman ya farke a minti na 26.

Fajardo ya zura ƙwallo da ta bai wa Panama nasara da ci 2-1 a minti na 83.

Weah ya fitar da wata sanarwa ta kafafan sada zumunta, inda ya bayar da haƙuri tare da neman gafarar waɗanda ya ɓata wa rai.

Yanzu haka dai Amurka, wacce ita ce ke karɓar baƙuncin gasar cin kofin na Copa America, muddin tana son zuwa zagaye na gaba to dole ne ta yi nasara a wasanta da Uruguay da zura ƙwallaye wanda ko da Panama ta yi nasara kan Bolivia za ta samu tsallake wa.

Continue Reading

Kasashen Waje

An tafka muhawarar farko tsakanin shugaba Biden da Trump

Published

on

An tafka muhawarar farko tsakanin shugaba Biden da Trump

An tafka muhawarar farko tsakanin shugaba Biden da Trump

Shugaban Amurka Joe Biden da tsohon shugaban ƙasar Donald Trump sun gwabza muhawara a daren Alhamis, inda suka fafata kan tattalin arziƙin Amurka da harkokin ƙasashen waje da haƙƙin zubar da ciki da kuma batun ƙaura daga kan iyakar Mexico zuwa Amurka.

“Muna tamkar a wata matalauciyar ƙasa a duniya kuma abin kunya ne,” in ji Trump ya faɗa yayin muhawarar da aka watsa ta talabijin ga ƙasa baki ɗaya, daga hedkwatar gidan talabijin na CNN da ke Atlanta.

“Ba a mutunta mu,” in ji Trump, yana zargin Biden. “Suna tunanin mu wawaye ne.”

Biden ya mayar da martani lokaci guda, yana kallon Trump. Tare da cewa “Wannan shi ne shugaban ƙasa mafi muni a tarihin Amurka. Wannan mutumin bai san ma’anar dimokuraɗiyyar Amurka ba.”

Haɗuwar Biden-Trump, watanni huɗu gabanin zaɓen ranar 5 ga watan Nuwamba, ita ce muhawara ta farko da aka taɓa yi a zagaye na huɗu na zaɓen shugaban ƙasar Amurka.

Hakanan sake haɗuwa ne tun muhawarar su guda biyu a shekarar 2020, wanda ya faru a cikin watanni biyu kafin Biden ya kayar da yunƙurin sake zaben Trump na wa’adi na biyu a Fadar White House.

Muhawarar ta ranar Alhamis ita ce karo na farko da shugabannin Amurka biyu suka taɓa yin muhawara a tsakaninsu, kuma shi ne karo na farko, da Biden da Trump suka haɗu a ɗaki ɗaya tun bayan muhawarar da suka yi a watan Oktoban 2020.

KU KUMA KARANTA:Biden ya yi alƙawarin kare Isra’ila daga harin ramuwar gayya na Iran

Trump ya tsallake bikin rantsar da Biden a watan Janairun 2021, kuma tun daga lokacin suka yi ta zage-zage da juna, ciki har da matakin muhawara a daren Alhamis.

A cikin ‘yan kwanakin nan, Trump ya yi ba a game da shirye-shiryen muhawarar Biden, inda ya ba da shawarar cewa zai bukaci ƙarin ƙarfi daga likita don samun damar iya muhawarar ta mintuna 90, gaba da gaba.

Trump ya faɗa wa wani gangamin magoya baya a Philadelphia cewa, “A yanzu haka, Joe ya tafi gidan katako don yin nazari,” yayin da yake zayyana alamomi da hannunsa. “Yanzu yana barci, saboda suna son ya samu ƙarfi.”

Continue Reading

Kasashen Waje

Kotun duniya ta umurci Isra’ila ta dakatar da kai farmaki a Rafah

Published

on

Kotun duniya ta umurci Isra’ila ta dakatar da kai farmaki a Rafah

A ranar Juma’a ne babban kotun duniya ICJ ta umarci Isra’ila da ta dakatar da hare-haren da take yi a Rafah, birnin da ke kudancin Gaza inda Falasɗinawa sama da miliyan ɗaya suka nemi mafaka a cikin mawuyacin hali.

Ko da yake da wuya Isra’ila ta bi wannan umarni, wanda babbar kotun Majalisar Ɗinkin Duniya ba ta da hurumin aiwatar da shi, amma hukuncin da aka yanke zai ƙara matsin lamba kan ƙasar.

A ci gaba da ƙalubalantar ɓacin ran da ƙasashen duniya suka yi kan rikicin jin kai a yankin, sojojin Isra’ila sun ci gaba da kai munanan hare-haren da suka ƙaddamar sakamakon hare-haren Hamas na ranar 7 ga watan Oktoba.

KU KUMA KARANTA:Babbar Kotun MƊD ta fara sauraron ƙara kan afka wa Rafah da Isra’ila ta yi

Tattaunawar tsagaita buɗe wuta ta ci tura, duk da matsin lamba da ake yi a gida na firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu na ganin an sako mutanen da a ka yi garkuwa da su a Gaza.

Umurnin na ICJ ya biyo bayan roƙon gaggawa da ƙasar Afirka ta Kudu ta gabatar a wani ɓangare na shari’ar da take ci gaba da yi a kotun da ke birnin Hague na ƙasar Netherlands, inda ta zargi Isra’ila da aikata kisan kiyashi a hare-haren da ta shafe watanni ana kai wa Gaza, zargin da Isra’ila da Amurka suka musanta.

Mai yiyuwa ne shari’ar za ta ɗauki shekaru ana warwarewa, amma Afirka ta Kudu ta nemi umarnin wucin gadi don kare Falasɗinawa.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like