Connect with us

Ɗalibai

Hukumar JAMB ta sake ɗage jarabawar wasu ɗalibai a cibiyar Kaduna

Published

on

Hukumar Shirya Jarrabawar Shiga Jami’a ta JAMB, ta sake sanya ranar rubuta jarabawar gama-gari ta Jami’a, UTME, ga wasu ‘yan ɗalibai a Kwalejin Christ Ambassadors da ke Sabon Tasha, Kaduna Centre, sakamakon matsalar na’ura.

Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya ya bayar da rahoton cewa, ‘yan takara da dama sun ka sa zana jarrabawar a cibiyar a ranar Talata, lamarin da ya haifar da ƙorafi daga wasu ‘yan takarar da iyayensu.

Wakilin Kamfanin Dillancin Labarai na NAN da ya sa ido a kan jarabawar a ranar Laraba, ya ruwaito cewa ɗalibai 150 ne kawai suka rubuta jarabawar a rukunin farko, kuma 100 kowannensu a mataki na biyu da na uku.

KU KUMA KARANTA: Hukumar NSCDC ta tura jami’ai 422 don sanya ido kan UTME a Kano

Wannan ya kai ɗalibai 350 saɓanin 750 a kowace rana, inda ake sa ran ɗalubai 250 ne za su rubuta jarabawar kowane rukuni. Ɗaya daga cikin ɗaliban, Francis Patrick, ya shaida wa NAN cewa ya shirya rubuta jarabawar da misalin ƙarfe 12 na rana a ranar 25 ga Afrilu.

Patrick, ya ce har zuwa ƙarfe 12:00 na rana, waɗanda ya kamata su rubuta jarrabawar da ƙarfe 6:00 na safe da 9:00 na safe, har yanzu suna rubutawa saboda ba su fara kan lokaci ba.

“Mun kuma samu labarin cewa wasu kwamfutocin na fitar da wasu ɗaliban yayin da suke da sauran lokacin kammala jarrabawar. “Na tsaya har ƙarfe 6:00 na yamma. kuma daga ƙarshe ya ka sa rubuta jarrabawar.

Na zo da safe ne kawai aka ce wasu daga cikinmu da ba su iya rubutawa jiya an nemi su miƙa takardar jarrabawarsu. “Yanzu, ban san abin da zan yi ba,” in ji shi.

Wata ɗalibar, Veronica Isuwa, ta ce ya kamata ta rubuta jarabawar da ƙarfe 9:00 na safe, amma an sake sanya ranar gobe. Ita ma wata ɗalibar Debora Eze ta shaida wa NAN cewa ya kamata ta zana jarrabawar ranar Laraba da ƙarfe 12:00 na rana. amma an gaya musu cewa tsarin zai iya ɗaukar ɗalibai 100 kawai.

“Sun nemi mu jira ƙarin umarni, don haka muna jira”, in ji ta. Da take mayar da martani kan batun, shugabar JAMB a cibiyar, Balkisu Abdullahi, ta bayyana wa NAN cewa uwar garken ba ta iya ɗaukar kwamfutoci 250 a lokaci guda, kamar yadda aka tsara.

Misis Abdullahi ta ce an buƙaci ɗalibai da ba su yi jarrabawar a rana ta ɗaya da ta biyu ba, da su gabatar da fom ɗin jarrabawar domin baiwa JAMB damar sake jadawalin jarabawar zuwa wata rana.

Ta yi nadamar matsalar da aka samu a na’ura, inda ta ƙara da cewa JAMB na haɗa kai da hukumar gudanarwar cibiyar domin shawo kan lamarin, kamar dai yadda ta tabbatar wa iyaye cewa babu wani yaro da zai faɗi jarrabawar.

Ta shawarci iyaye da su riƙa yiwa ‘ya’yansu tarbiyya tare da cusa musu tarbiyya mai kyau, inda ta ce zuwa jarabawa da wuƙaƙe abu ne da bai dace ba.

“Abin da ya faru a ranar Talata yana da ban tsoro yayin da wasu daga cikin ’yan takarar ke riƙe da wuƙaƙe suna yi mana barazana a lokacin da muke bayyana matsalolin na’urar da abin da muka yi niyyar yi don gyara lamarin.

Ta ƙara da cewa “Iyayen kuma ba su taimaka lamarin ba, maimakon su kwantar da hankalin ‘ya’yansu, wasu daga cikinsu suna ihu da babbar murya, suna barazanar ɗaukar matakin shari’a a kan hukumar ta JAMB.”

A nata ɓangaren, Manajan Makarantar, Tosin Akinpeloye, ta bayyana cewa an samu matsala a na’ura ne saboda an inganta uwar garken JAMB ta yadda za ta yi aiki mai kyau a kan kwamfutoci da na’urorin sarrafa Co i7.

Mis Akinpeloye ta ce cibiyar kwamfuta ta makarantar tana da kwamfutoci 260 da kwamfutocin tebur guda 20 amma suna aiki a kan na’urori masu sarrafa kwamfuta na Co i5, inda ta ce an kawo na’urar da za ta ɗauki dukkan kwamfutocin.

“Ina tabbatar muku cewa dukkan ɗaliban da za su rubuta jarrabawar ranar Alhamis za su yi hakan ba tare da wata matsala ba,” in ji ta. Sai dai lamarin ya sha bamban a cibiyar Jami’ar Jihar Kaduna, inda kodinetan JAMB, Benedict Opke, ya ce kayayyakin suna aiki yadda ya kamata.

Ɗaya daga cikin ɗaliban a cibiyar, Favour Bamiboye mai shekaru 15 da ke son zama likita, ta ce jarrabawar ta tafi lami lafiya ba tare da wata matsala ba. Hakazalika, wasu daga cikin ɗaliban da suka rubuta jarabawar a cibiyar kwalejin Queen Amina, sun yabawa JAMB, da kuma hukumar gudanarwar makarantar bisa gudanar da aikin ba tare da tangarɗa ba.

“Wannan shi ne karon farko da nake rubuta jarabawar UTME, kuma abin ya burge ni saboda komai ya tafi lami lafiya,” in ji ɗaya daga cikin ɗaliban a cibiyar, Hafsat Abubakar.

1 Comment

1 Comment

  1. Pingback: Ɗaliban da suka zana jarabawar JAMB, su fara duba sakamakon daga yau talata – JAMB | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Ɗalibai

Sai da aka kashe na’urorin ɗaukar hoto kafin a sace ɗaliban Kogi – Gwamna Ododo

Published

on

Rahotanni daga jihar Kogin Najeriya na cewa an kashe duka na’urorin ɗaukan hoto a jami’ar kimiyya da fasaha ta Confluence University da ke jihar kafin a sace wasu ɗaliban makarantar a cewar Gwamna Usman Ododo.

A ranar Alhamis wasu ‘yan bindiga suka kutsa jami’ar wacce ke Osara suka sace ɗalibai tara cikin dare.

Ya zuwa lokacin haɗa wannan rahoto ba a ji ɗuriyar ɗaliban ko waɗanda suka sace su ba.

Ododo ya bayyana hakan ne yayin da ya kai ziyarar ganewa idonsa jami’ar a ranar Asabar.

“Binciken da muka gudanar ya zuwa yanzu, ya nuna cewa, duka na’urorin da muka saka an kashe su, kuma wannan ba wani abu ba ne illa zagon ƙasa daga mutanen cikin gida.” Ododo ya ce.

Gwamna Ododo ya yi ƙira ga iyayen ɗaliban da su kwantar da hankulansu saboda jami’an tsaro suna bin diddigin al’amarin yana mai cewa buƙatar gwamnati a yanzu shi ne a ceto ɗaliban.

KU KUMA KARANTA:Muna ƙoƙarin kuɓutar da ɗaliban jami’ar da ‘yan bindiga suka sace – Gwamnatin Kogi

Batun satar ɗalibai a makarantun firaimare da sakandare da ma jami’o’i a Najeriya ba baƙon abu ba ne musamman a arewaci.

‘Yan bindiga kan sace ɗalibai da dama su kutsa da su cikin daji har sai an biya kuɗin fansa kafin a sako su.

Satar mutane domin neman kuɗin fansa, babbar matsala ce a mafi akasarin jihohin arewa maso yammacin Najeriya.

Hukumomin ƙasar sun ce suna iya bakin ƙoƙarin su wajen ganin sun kawo ƙarshen wannan al’amari.

Continue Reading

Ɗalibai

Za’a a fara koyar da harsunan Ijaw, Faransanci, da Sinanci a makarantun a jihar Bayelsa

Published

on

Daga Maryam Umar Abdullahi

Gwamnatin Bayelsa ta ce za ta ba da fifiko kan koyo da koyar da harsunan Ijaw, da Faransanci, da kuma Sinanci a makarantun gwamnati a jihar.
Mataimakin gwamnan jihar, Mr. Lawrence Ewhrudjakpo ya bayyana a cikin wata sanarwa da babban mai taimaka masa na musamman kan harkokin yaɗa labarai, Doubara Atasi, ya fitar a jiya Alhamis cewa, ƙaruwar tasirin tattalin arziƙin ƙasar China a harkokin duniya a matsayinta na babbar jigo a harkokin cinikayya da cinikayyar duniya, ya nuna kamatar tabbatar da shigar da ƙarshen ƙasar China a cikin manhajar karatu.

KU KUMA KARANTA: Firaiministan Nijar, Lamine Zeine, ya caccaki ECOWAS  kan yin zagon ƙasa

Ewhrudjakpo ya bayyana cewa, gwamnati za ta fi maida hankali kan harsunan ne domin, baya ga muhimman darussa na kimiyya, harsunan za su taimaka wajen samar da yaran da za su ci gajiyar damar sana’ar da waɗannan darussa ke bayarwa a nan gaba.

Ana magana da harshen Ijaw ne a yankin Niger-Delta da ya ƙunshi jihohin Delta, Bayelsa da kuma Cross Rivers. Akwai kuma waɗannan suke harshen da ake ƙira “Arogbo-Ijaw” a jihar Ondo.

A shekarun nan, masana na jadada buƙatar ganin gwamnatoci sun ɗauki matakan raya al’adu da harsuna da ake gani aka kara watsi da su sabili da ci gaba na zamani.

Continue Reading

Ɗalibai

A bawa ɗalibai tallafin karatu, ba bashin kuɗin karatu ba – ƙiran ASUU ga gwamnatin tarayya

Published

on

Ƙungiyar malaman jami’o’i ta Najeriya (ASUU) ta buƙaci Shugaba Bola Tinubu ya sauya dokar ba da bashin karatu ga ɗalibai da ya amince da ita, zuwa tallafin karatu domin bai wa ɗalibai masu ƙaramin ƙarfi damar samun ilimi mai zurfi.

A wata hira da gidan Talbijin na Channels ranar Lahadi, shugaban ASUU ya ce bashin karatun ba abu ne mai yiwu ba. A cewarsa, bayar da bashi don yin karatu “ba zai ɗore ba”.

Farfesa Emmanuel Osodeke ya ce, “tunanin bayar da bashin karatu ga ɗalibai ya zo ne a 1972 kuma yana cikin harkokin bankuna da aka kafa”.

KU KUMA KARANTA: NURTW ta goyi bayan shugaba Tinubu kan cire tallafin man fetur

Ya yi iƙirarin cewa mutanen da suka karɓi bashin, ba su taɓa biya ba, kuna iya zuwa ku bincika. A shekarar 1994 ko 1993, sojoji sun kafa dokar soja mai lamba inda suka kafa hukumar bayar da bashi ga ɗalibai. Sai Majalisar dokoki ta daidaita ta a shekara ta 2004 kuma a cikin shekara ɗaya, ta wargaje. Kuɗaɗen suka ɓace. Muna so mu ga yadda wannan zai bambanta”.

A cewarsa, akwai ɗalibai sama da miliyan ɗaya a jami’o’in gwamnatin Najeriya kuma rancen ba zai iya biyan kuɗin karatun ɗalibai ba.

A ranar Litinin ne Shugaba Tinubu ya sa hannu a kan dokar ba da bashi ga ɗalibai domin cika alƙawarin da ya ɗauka a lokacin yaƙin neman zaɓensa.

Shugaban majalisar wakilai ta 9, Femi Gbajabiamila, wanda yanzu shi ne shugaban ma’aikatan fadar shugaban ƙasa ne ya ɗauki nauyin gabatar da ƙudurin dokar a majalisa.

Dokar ta tanadi ba da bashi maras ruwa ga ɗalibai masu ƙaramin ƙarfi a Najeriya.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like