Connect with us

Doka

Gwamnatin tarayya na la’akarin hana amfani da baburan achaɓa a ƙasa baki daya

Published

on

Gwamnatin tarayya ta ce tana tunanin sanya dokar hana amfani da babura da aka fi sani da okada. Babban Lauyan Gwamnatin Tarayya (AGF) kuma Ministan Shari’a, Abubakar Malami, ne ya sanar da hakan a ranar Alhamis din da ta gabata yayin da yake zantawa da manema labarai a fadar shugaban ƙasa. Wannan ya faru ne bayan kammala taron majalisar tsaro ta ƙasa (NSC), da shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ya jagoranta a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja.

Ministan ya ce bincike ya nuna cewa ana amfani da Achaɓa wajen aikin haƙar ma’adinai a fadin ƙasar kuma haramcin na iya katse hanyoyin samun kuɗaɗen ‘yan ta’adda da ‘yan fashi. Malami ya ce taron ya mayar da hankali ne kan kayan aikin da ‘yan ta’addan ke amfani da su wajen dakatar da ayyukansu. Ya ce akwai buƙatar gwamnati ta dauki matakin saboda ‘yan ta’adda sun ƙaura daga hanyoyin da suka saba amfani da su wajen gudanar da ayyukansu zuwa haƙo ma’adinai da karbar kudin fansa.

Ministan ya ce ’yan fashin ne ke amfani da baburan wajen safara, yayin da hakar ma’adanai ke ba su kuɗaɗen da za su samu kuɗin sayen makamai.

Dangane da ko gwamnati za ta yi la’akari da illar hana babura da ayyukan hakar ma’adinai ga talakawan Najeriya da tattalin arzikin ƙasar, ministan ya ce gwamnatin tarayya za ta fifita buƙatun ƙasa da na jama’a fiye da buƙatun mutum daya.

Shima da yake magana, Ministan Harkokin Cikin Gida, Rauf Aregbesola, ya ce an yi ƙoƙari sosai wajen tattara bayanan sirri kafin harin baya-bayan nan da aka kai a Cibiyar Gyaran hali na Kuje, amma ya yi nadamar cewa babu wani shiri da za a yi a kai.

Aregbesola wanda ya ce an mika rahoton farko na bincike kan harin ga shugaban ƙasar, ya ba da tabbacin cewa za a bayar da cikakken rahoto a ƙarshen binciken. Ya ce za a hukunta wadanda aka samu sun yi watsi da aikinsu.

1 Comment

1 Comment

  1. Pingback: Dalilin da yasa mahaya okada a Kubwa suka daina karɓar sabbin takardun naira | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Doka

Kotu ta umarci jihar Ondo da ta biya diyyar naira miliyan 30 ga mutumin da ‘yan Amotekun suka harbe

Published

on

Ta kama mijinta yana lalata da ’ya’yan cikinsu

Wata babbar kotun Ondo da ke zamanta a Akure, a ranar Larabar da ta gabata ta umarci gwamnatin jihar Ondo da ta biya wani Oluwasegun Oluwarotimi kuɗi naira miliyan 30 a matsayin diyyar harbin bindiga da ya samu a wata arangama da jami’an tsaro na jihar, wanda aka fi sani da ‘yan Amotekun.

Oluwarotimi mai shekaru 36, mai tuƙa babur ne, wato ɗan okada ne lokacin da lamarin ya faru.

A nasa jawabin, Mai shari’a Adejumo ya bayar da umarnin a biya Oluwarotimi kuɗi naira miliyan talatin a matsayin diyya.

KU KUMA KARANTA: Hukumar NYSC ta biya diyya ga dangin ɗan bautar ƙasa da ya ɓata

Oluwarotimi, wanda a yanzu an yanke shi ne sakamakon harbin da aka yi masa ba bisa ka’ida ba,inda ya shigar da karar a gaban kotu.

“B bisa ka’ida ba a titin Araromi a ranar 9 ga watan Agustan 2021 a Akure, harbin da Amotekun ta yi ya saɓa wa hakkin ɗan Adam.

“Kotu ta umurci waɗanda ake ƙara da su hada kai su biya Naira miliyan 20 ga wanda ake kara a matsayin diyya na gaba daya da kuma Naira miliyan 10 a matsayin diyya ta misali,” in ji alkalin.

Continue Reading

Doka

An sanya dokar hana fita a Kano

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta sanya dokar ta-ɓaci har zuwa faɗuwar rana don kaucewa taɓarɓarewar doka da oda, biyo bayan tattara sakamakon zaɓen gwamna da na ‘yan majalisar dokokin jihar.

Kwamishinan yaɗa labarai da harkokin cikin gida na jihar, Malam Muhammad Garba ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar da safiyar Litinin.

KU KUMA KARANTA: Yadda Abba Kabir Yusuf na NNPP ya lashe zaɓen Kano

Ya ce an yanke shawarar ne don hana ’yan daba su haifar da hargitsi a halin da ake ciki.

Kwamishinan ya yi kira ga jama’ar jihar da su kasance a cikin gida domin jami’an tsaro ba za su ƙyale kowa ko wata ƙungiyar da ke da niyyar haddasa fitina ba.

Continue Reading

Doka

Kotu ta sanya sharudɗa akan batun bada belin doguwa

Published

on

sharudɗan sune kamar haka:

Kotu ta haramtawa Alhassan Ado Doguwa zuwa mazaɓarsa ranar zaɓen ta gwamna da ‘yan majalisar jiha.

Wannan dai na cikin sharudɗa da babbar kotun tarayya ta sanya kafin bada belin Alhassan Ado Doguwa.

Ga dai ƙarin jerin sharudɗan da kotu ta sanya kafin bada belin.

1- Zai ajiye zunzurutun kuɗi har naira miliyan 500

2- Gabatar da sarki mai daraja ta ɗaya a matsayin wanda zai tsaya mishi.

KU KUMA KARANTA: INEC ta cire sunan shugaban masu rinjaye, Doguwa daga jerin sunayen ‘yan majalisar wakilai

3- Gabatar da babban sakatare a gwamnatin jiha ko ta tarayya a matsayin wanda zai tsaya mishi.

4- Zai ajiye Fasfo da sauran dukkanin takaddunshi na tafiya a kotu.

A karshe kuma kotu tace bazai halacci mazaɓarsa ba yayin zaɓen gwamna da yan majalisun jiha dake tafe.

Ko ya kuke kallon wannan batu?

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like