Gwamnatin tarayya na la’akarin hana amfani da baburan achaɓa a ƙasa baki daya

1
664

Gwamnatin tarayya ta ce tana tunanin sanya dokar hana amfani da babura da aka fi sani da okada. Babban Lauyan Gwamnatin Tarayya (AGF) kuma Ministan Shari’a, Abubakar Malami, ne ya sanar da hakan a ranar Alhamis din da ta gabata yayin da yake zantawa da manema labarai a fadar shugaban ƙasa. Wannan ya faru ne bayan kammala taron majalisar tsaro ta ƙasa (NSC), da shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ya jagoranta a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja.

Ministan ya ce bincike ya nuna cewa ana amfani da Achaɓa wajen aikin haƙar ma’adinai a fadin ƙasar kuma haramcin na iya katse hanyoyin samun kuɗaɗen ‘yan ta’adda da ‘yan fashi. Malami ya ce taron ya mayar da hankali ne kan kayan aikin da ‘yan ta’addan ke amfani da su wajen dakatar da ayyukansu. Ya ce akwai buƙatar gwamnati ta dauki matakin saboda ‘yan ta’adda sun ƙaura daga hanyoyin da suka saba amfani da su wajen gudanar da ayyukansu zuwa haƙo ma’adinai da karbar kudin fansa.

Ministan ya ce ’yan fashin ne ke amfani da baburan wajen safara, yayin da hakar ma’adanai ke ba su kuɗaɗen da za su samu kuɗin sayen makamai.

Dangane da ko gwamnati za ta yi la’akari da illar hana babura da ayyukan hakar ma’adinai ga talakawan Najeriya da tattalin arzikin ƙasar, ministan ya ce gwamnatin tarayya za ta fifita buƙatun ƙasa da na jama’a fiye da buƙatun mutum daya.

Shima da yake magana, Ministan Harkokin Cikin Gida, Rauf Aregbesola, ya ce an yi ƙoƙari sosai wajen tattara bayanan sirri kafin harin baya-bayan nan da aka kai a Cibiyar Gyaran hali na Kuje, amma ya yi nadamar cewa babu wani shiri da za a yi a kai.

Aregbesola wanda ya ce an mika rahoton farko na bincike kan harin ga shugaban ƙasar, ya ba da tabbacin cewa za a bayar da cikakken rahoto a ƙarshen binciken. Ya ce za a hukunta wadanda aka samu sun yi watsi da aikinsu.

1 COMMENT

Leave a Reply