Connect with us

Labarai

Gwamna Abba ya ƙaddamar da kwamitocin bincike kan rikicin siyasa da ta’annati da dukiyar Kano

Published

on

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya ƙaddamar da kwamitocin biyu da za su yi bincike kan ta’annati da dukiyar al’umma, da mutanen da suka bata da rikicin siyasa da suka afku a tsakanin 2015 da 2023.

A yayin da yake ƙaddamar da kwamitocin a ranar Alhamis, Gwamna Yusuf ya yi alkawarin hukunta duk wanda aka samu da laifi.

Wata sanarwa da kakakin gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya fitar ta ambato Gwamna Yusuf yana tunatar da cewa bincike kan ta’annati da dukiyar al’umma wani bangare ne na alkawarin da ya yi a lokacin da ake rantsar da shi.

Ya ƙara da cewa za a binciko tare a hukunta masu hannu a rikicin siyasa a jihar Kano musamman a zaɓukan 2023.

Sanarwar ta ruwaito gwamnan na cewa “Rikicin siyasa babban ƙalubale ne ga dimokuraɗiyya a duniya baki ɗaya. Yana janyo asarar rayuka da dukiya, da ma janyo al’umma su ki amincewa da wadanda ke jagorantar su.”

“Munanan kashe-kashen da aka yi na siyasa musamman a 2023 ba za su tafi haka kawai ba, za a dauki matakin ne don hana afkuwar hakan a nan gaba,” a cewar gwamnan.

Kwamitin farko wanda yake karkashin Mai Shari’a Zuwaira Yusuf zai mayar da hankali kan rikicin siyasa da mutanen da suka bata tun daga 2015 zuwa 2023.

KU KUMA KARANTA: An haramta shirya fina-finan da ke nuna ƴan daudu da ƴan daba a Kano

Gwamna Abba ya ce “Muna sa ran za su binciki munanan ayyukan, sannan su zakulo wadanda suke daukar nauyin rikicin. Su nemo tushen rikicin, sannan su gano yadda aka kitsa rikici a 2015, 2019 da 2023.”

Da yake ƙaddamar da kwamiti na biyu ƙarƙashin Mai Shari’a Faruk Lawan, Gwamna Abba ya dora wa kwamitin alhakin gudanar da bincike kan ta’annati da dukiya da kadarorin al’umma.

Munanan kashe-kashen da aka yi na siyasa musamman a 2023 ba za su tafi haka kawai ba, za a dauki matakin ne don hana afkuwar hakan a nan gaba

Ya bukaci Ma Shari’a Lawan da dukkan mambobinsa kan kada su yi shayin bayyana duk wani waje da aka yi almundahana da dukiya ko ƙadarar al’ummar a lokacin mulkin gwamnatin da ta gabata a ciki da wajen jihar Kano.

Gwamnan ya kuma jaddada cewa wannan mataki ba shi da alaka da siyasa ko nufar wasu mutane, aiki ne da ya dace da buktun jama’ar jihar Kano.

A yayin da yake kira ga kwamitocin da kar su kuskura su hada baki da wani, Gwamnan na Kano Yusuf ya kuma bukace su da su riƙe amana da aiki da rantsuwar da suka yi ta gudanar da aiki da gaskiya don yin adalci a jihar.

Gwamnan ya ce sai da aka yi tantancewa sosai kafin a zaɓi mambobin kwamitocin, kuma ya yi amanna za su yi aikin kamar yadda ake zato.

Ya ce “Mun yi duba ga tarihin ayyukanku, kuma ba mu samu wani daga cikin ku da rashin kirki ba. Mun amince da ku kuma muna fatan za ku mika rahotanninku a cikin watanni uku.”

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

'Yansanda

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

Published

on

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

Rundunar ’yan sandan Najeriya ta tube wa wasu jami’an ta biyar kaki sakamakon zargin su da karɓar cin hancin kuɗi kimanin Naira miliyan uku.

Mataimakin Shugaban ’yan Sanda mai kula da Shiyya ta shida ta da ke Jihar Kuros Riba, Jonathan Towuru, ya sanar a Kalaba cewa ’yan sandan sun kwace kuɗin ne da bakin bindiga a hannun wani mai abin hawa.

A makon jiya ne aka zargi jami’an da ƙwayar kuɗin da bakin bindiga a hannun wani mutum da rundunar ta sakaya sunansa.

Yanzu haka waɗanda ake zargin an tuɓe masu kaki amma ana tsare da su ana bincike, da zarar an same su da laifi kotu za a turasu ta yanke masu hukuncin da ya dace.

KU KUMA KARANTA: ’Yan sanda za su tantance ’yan banga a Yobe

Mataimakin shugaban ’yan sandan ya ce waɗanda ake zargin su da karɓar cin hancin kuɗi Naira milyan uku daga wannun wani.

Ko a kwanan baya irin haka ta taba faruwa a kan babbar hanyar Kalaba zuwa Ikom inda aka kama wasu ’yan sanda kan karbar na goro.

Tafiya a kan hanyar na yawan zargin ’yan sanda da kula da shingen bincike a kan hanyar da yawan tatsar su kuɗi.

Continue Reading

Labarai

Ƙaramar Hukumar Kwami ta kafa kwamitin tsaro saboda rikicin manoma

Published

on

Ƙaramar Hukumar Kwami ta kafa kwamitin tsaro saboda rikicin manoma

Ƙaramar Hukumar Kwami ta kafa kwamitin tsaro saboda rikicin manoma

A ƙoƙarinsa na kauce wa rikicin manoma da makiyaya da ke yawan faruwa a lokacin damuna, Shugaban Karamar Hukumar Kwami a Jihar Gombe, Dakta Ahmed Wali Doho, ya kafa kwamitin tsaro da sanya ido kan ɓangarorin.

Da yake zantawa da manema labarai a ofishinsa da ke garin Malam Sidi, shugaban karamar hukumar, ya bukaci manoma da su guji noma burtalolin shanu, wanda hakan ke haifar da rikici tsakaninsu da makiyaya, da ke haifar da asarar rayuka.

Su ma makiyayan ya gargade su da cewa su guji shiga gonakin manoma, saboda hakan ne ke jawo rikici idan suka cinye musu amfanin gona.

A cewarsa, lokacin girbi me aka fi samun rikicin manoma da makiyayan, saboda haka kwamitin zai ci gaba da sa ido daga yanzu har zuwa lokacin girbin don ganin ba a samu rikici ba.

KU KUMA KARANTA: Gwamna Yusuf ya amince da sayen taki na naira biliyan 5 don manoman Kano

Ya ƙara da cewa, kusancin garin Kwami da rafi ya sa ya zama wuri mai kyau don noman rani.

Don haka ya ja hankalin manoman yankin da su yi amfani da wannan damar wajen bunkasa tattalin arzikinsu.

Ya jaddada cewa noman rani na da matukar muhimmanci wajen magance matsalar karancin abinci a Najeriya.

Hakan ne ya sa suka haɗa kan matasan yankin don su fara noman rogo da zai taimaka wajen shawo kan matsalar ƙarancin abinci da rage wa manoma tsadar takin zamani.

Continue Reading

Labarai

’Yan sanda za su tantance ’yan banga a Yobe

Published

on

’Yan sanda za su tantance ’yan banga a Yobe

’Yan sanda za su tantance ’yan banga a Yobe

Rundunar ’yan sandan jihar Yobe ta ƙaddamar da shirin yin gyara da kuma tantance ’yan banga domin kawar da ɓata-garin cikin

Rundunar ’yan sandan jihar Yobe ta ƙaddamar da shirin yin gyara da kuma tantance ’yan banga domin kawar da bata-gari a cikinsu.

Kwamishin ’yan sandan jihar, Garba Ahmed, ya sanar da shirin bayan an kama wasu ’yan banga uku da aikata manyan laifuka.

Ya jaddada muhimmancin sake duba ayyukan ’yan banga a jihar, duk da  muhimmiyar rawar da suke takawa wajen taimaka wa jami’an tsaro a yaki da miyagun laifuka.

Ya ce yin gyaran da kuma tantancewa ya zama dole sakamakon ƙorafe-ƙorafen neman yin hakan daga jama’a.

Ya bayyana cewa jama’a sun yi ƙiran ne bayan kama wasu ’yan banga uku da laifin hada baki wajen shiga gida, sata, ƙwace da kuma sayar da kayan sata a Damaturu.

Wata sanarwa da DSP Dungus Abdul Karim, kakakin rundunar, ya fitar, ta ce wasu daga cikin ’yan banga sun kai korafi bayan faruwar lamarin.

KU KUMA KARANTA: Ƴan bindiga sun kashe mutum 12 a Kaduna, sun kai hari a ofishin ƴan sanda a Zamfara

“A ranar 27 ga watan Yuni, 2024, rundunar ta amsa kiran wani mai shago a Damaturu, wanda ya dauki ’yan banga aikin gadi, amma suka kwashe kayan shagon na makudan kudade ba tare da bayani ba.

“Bincike ya kai ga kama wasu mutane biyu da kayan sata da ake zargin sun saya ne daga wani dan banga wanda nan take aka kama shi.

“Ana shawarta jama’a da su yi taka-tsan-tsan wajen daukar masu gadi, sannan su kai rahoton ’yan banga da aka ga suna aikata laifi a bakin aikinsu.”
Sanarwar ta ci gaba da cewa, rundunar tana ɓullo da tsare-tsare don daukar bayanan ’yan banga domin sa ido kan ayyukansu.

Ta ci gaba da cewa ofisoshin ’yan sanda na yankuna da ke jihar za su jagoranci wannan aikin tantancewan domin kawar da baragurbi a cikin ’yan banga.

“Don  haka ake ƙira ga jama’a da su ci gaba da tallafa wa ’yan sanda wajen jainrahoton ayyukan jami’an tsaron da ba su dace ba a hedkwatar jihar ta lamba 07068858500, ko kuma a gabatar da wasikar korafin ga kwamishinan ’yan sanda  ta hanyar kakakin rundunar,” in ji sanarwar.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like