Connect with us

Labarai

Daraktan Galaxy, Farfesa Muhammad Bello ya taya Ministan Sadarwa Pantami murnar samun lambar Yabo ta CIISec

Published

on

Farfesa Muhammad Bello Abubakar, Manajan Darakta na Cibiyar Galaxy Backbone, ya taya babban Ministan Sadarwa Zamani da tattalin arziki na Najeriya Farfesa Isah Ali Ibrahim Pantami murnar samun lambar yabo ta (CIISec) Charted Institute of Information Security.

Farfesa Muhammad Bello Abubakar, ya aika da saƙon taya Ministan Murnar ne ta wajen mai taimaka masa na musamman a bangaren yaɗa labarai Tasiu Muhammad Pantami, inda yace Ministan ya cancanci fiye da haka.Yace wannan lambar yabo Minista Pantami, yana cikin mutane 89 a duniya da suke da wannan lambar su yan kasar Afirka basu da yawa.

A cewar Tasiu Pantami, MD Galaxy, ya bayyana Ministan ne da haziƙin Minista wanda ya kawowa wa ƙasar sa ci gaba mai ma’a a bangaren sadarwar zamani tun shigar ofis a matsayin Ministan Najeriya wanda ya maida hankali sosai akan abunda ya shafi harkar tsaron kasa ta bangaren kimiyya da hakan kuma ya haifar da ‘Da mai Ido.

Farfesa Muhammad Bello Abubakar, ya yabawa cibiyar CIISec na yadda suka zakulo Farfesa Isa Ali Ibrahim Pantami Ministan sadarwa ganin yadda ya mayar da hankali wajen ci gaban kasa da kula da harkar sadarwar yanar gizo dan ci gaban duniya baki daya suka karrama shi da wannan lambar yabo.

Daga nan sai yace CIISec su kadai ne cibiyar kula da harkar sadarwa ingantacciya da suka samu izinin masarautar kasar Uk tun a shekara ta 2018 da aka daurawa alhakin kula da kwarewar harkar da ta shafi bangaren sadarwa kuma sune suka karrama Ministan.Sannan sai ya sake yin amfani da damar ya sake taya Ministan murna sosai saboda farin cikin da yake da shi wa Ministan.

2 Comments

2 Comments

  1. Pingback: Sau 66 wasu na ƙoƙarin yiwa Gwamnatin tarayya kutse – Pantami | Neptune Prime Hausa

  2. Pingback: Masana kimiyyar sadarwa sun yaba wa NCC kan samar da lambobin bai ɗaya | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like