Connect with us

Labarai

Boko Haram ta saki mata tara daga cikin sama da mutum 200 da ta sace a Najeriya  

Published

on

Boko Haram ta saki aƙalla ƴan gudun hijira tara daga cikin sama da 200 da ƙungiyar ta yi garkuwa da su a yankin Arewa maso Gabashin Najeriya, a cewar jami’ai a ranar Litinin.

Shugaban Hukumar Agajin Gaggawa ta Najeriya, NEMA, Barkindo Saidu ya ce an ga mutanen tara, waɗanda duka mata ne da ƴan mata, a sansanin ƴan gudun hijira na Ngala a jihar Bornon da ke arewa maso gabashin ƙasar.

“Ma’aikatan sansanin ƴan gudun hijirar sun ba da rahoton cewa mutum tara sun koma. An gan su a sansanin ƴan gudun hijirar,” kamar yadda Saidu ya shaida wa Anadolu ranar Litinin.

Sama da mata 200 da ƴan mata da maza, wadanda suka bar sansanin gudun hijirarsu don neman itace a Ngala da ke yankin arewa maso gabashin jihar Borno mayaƙan Boko Haram suka yi garkuwa da su.

Ƙungiyar yan ta’addan wacce ke da matsuguninta a yankin arewa maso gabashin Najeriya kana ta yi karfi a Chadi da Nijar da arewacin Kamaru da kuma Mali.

A ƴan shekarun nan, matsalar masu garkuwa da mutane da kuma yan fashi sun ɗaɗa ƙaruwa sosai a ƙasar da ke yankin Yammacin Afirka.

KU KUMA KARANTA: Mayaƙan Boko Haram sun sace mata 319 a Borno

Kimanin muyum 430 galibi mata da yara ne aka yi garkuwa da su a yankin arewacin ƙasar cikin ƴan makonni biyu da suka wuce.

Abubakar Boyi Sifawa, babban mai bincike a kan dabi’u da tsaro a Jami’ar Ilimi ta Shehu Shagari da ke arewa maso yammacin jihar Sakkwato, ya ɗora alhakin yawan sace-sacen jama’a da ƴan fashi da makami ke yi a kasar kan taɓarɓarewar tattalin arziki da talauci da rashin haɗin kai a tsakanin hukumomin tsaro.

“A bisa binciken da na yi, abin takaici, matasa da yawa a yanzu suna shiga ƙungiyoyin satar mutane da kuma masu ba da labari don a biya su saboda matsalar tattalin arziki, suna gaggawar su samu kuɗi saboda talauci, sannan suna fada wa cikin kungiyoyin ta’addanci bayan sun karɓa kuɗin fansa,” kamar yadda Boyi Sifawa ya shaida wa kamfanin dillacin labaran Turkiyya Anadolu.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like