Connect with us

Labarai

Ba zan yi amfani da kuɗin talakawa wajen neman tazarce ba – Abdullahi Sule

Published

on

Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule ya bada tabbacin cewa ba zai yi amfani da kobo ɗaya daga dukiyar jihar wajen yakin neman zaɓe a zaɓen 2023 ba.

Gwamnan ya bayar da wannan tabbacin ne a lokacin da yake jawabi a matsayin babban ɓako a wajen taron Karatun Ƙur’ani na kasa tare da bayar da tallafin kuɗi da ƙungiyar masu Karatun Ƙur’ani ta Najeriya ta shirya a ranar Lahadi.

“Ba zan yi amfani da dukiyar jihar nan wajen neman tazarce ko wani wa’adin mulki ba.

Ya bayyana cewa domin a samu saukin yaƙin neman zaɓensa, abokansa, abokan aikinsa da shugabannin da ya yi aiki da su a lokacin da yake sana’o’i ne suka haɗa masa kayan aiki a kwanan baya a wani ƙudiri da aka yi a Abuja, inda aka samu sama kuɗi Naira biliyan ɗaya da naira miliyan 200.

KU KUMA KARANTA ‘Yan sandan Kano sun kama mutum 7 da mallakar katin zaɓe ba bisa ƙa’ida ba

Yayin da yake jawabi a kan mimbari tare da kawo ayar Al Ƙur’ani mai tsarki, gwamnan Sule ya yi magana kan buƙatar ‘yan siyasa masu neman mulki suyi taka tsan-tsan don kada su zafafa harkokin siyasa.

“Allah yana ba da mulki ga wanda ya so, kuma a lokacin da yazo, kamar yadda ya bayyana a cikin Alkur’ani mai tsarki”

Gwamnan ya yi amfani da wannan dama wajen yin jawabi a kan buƙatar haɗa ƙarfi da ƙarfe wajen magance matsalar barace barace a kan tituna.

Ya ce akwai banbanci tsakanin mai bara da Almajiri, wanda shi mai neman ilimi ne, ya ce gwamnonin Arewa sun damu matuƙa kan yadda wasu iyaye ke tura ‘ya’yansu zuwa wurare masu nisa, galibi a faɗin jihohi, ba tare da sun yi shiri don kula da su ba, kuma yaron ba shi da wani abin da zai yi sai dai tsira ta hanyar bara.

“Babu wanda zai iya hana musulmi ‘yancin samun ilimi, sai dai iyaye su daina tura ‘ya’yansu ba tare da sun shirya biyan buƙatunsu na yau da kullun ba.

Gwamnan ya bada gudunmuwar naira miliyan goma sha uku domin gudanar da wannan asusu, sannan ya bayar da tallafin motoci guda biyu, ɗaya na ƙungiyar reshen jiha da na ƙungiyar a mataki na ƙasa.

1 Comment

1 Comment

  1. Pingback: Kasafin kuɗin 2023: Gwamna Sule zai fara aiki gadan-gadan | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like