Connect with us

Rasuwa

An yi jana’izar babban ɗan Gwamnan Nasarawa da Allah Ya yiwa rasuwa

Published

on

Gwamnan jihar Nasarawa Abdullahi Sule ya rasa ɗansa Hassan Sule wanda ya rasu a garin Lafia da yammacin ranar Alhamis, 26 ga watan Janairun 2023.

Marigayin wanda ya auri matarsa ​​ta farko, a watan Yunin shekarar da ta gabata, shi ne babban ɗan Gwamna Sule. Hassan mai shekaru 36.

Rasuwar ɗan gwamnan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da babban sakataren yaɗa labaran gwamnan, Ibrahim Adra ya rabawa manema labarai a ranar Juma’a. Sanarwar ta ce, “Mai Girma, Abdullahi A. Sule, Gwamnan Jihar Nasarawa, a madadin iyalansa, ya sanar da rasuwar ɗansa, Hassan Sule, wanda abin bakin ciki ne ya faru a ranar Alhamis 26 ga watan Janairu, 2023.

KU KUMA KARANTA:Allah Ya yima Dr. Goni Abba Kaka rasuwa

Hasan ya rasu yana da shekaru 36 a duniya. An yi jana’izar marigayi Hassan a Gudi da ke ƙaramar hukumar Akwanga a yau Juma’a da karfe 10 na safe.

Yayin da yake mishi addu’a

A halin da ake ciki, Shugaban zartarwa na karamar hukumar Akwanga, Safiyanu Andaha, ya bayyana matukar kaɗuwarsa da rasuwar ɗan gwamnan tare da jajanta wa iyalansa kan rasuwar Hassan.

“A madadin iyalaina, karamar hukumar Akwanga da al’ummar Mada land, ina so in mika sakon ta’aziyyarmu ga Gwamna Abdullahi Sule, da iyalansa da kuma ɗaukacin majalisar sarakunan gargajiya ta Gudi bisa wannan babban rashin.”

5 Comments

5 Comments

  1. Pingback: Sarkin Dutse HRH Alhaji Nuhu Muhammad Sanusi ya rasu a Abuja | Neptune Prime Hausa

  2. Pingback: Sarkin Dutse HRH Alhaji Nuhu Muhammad Sanusi ya rasu a Abuja - LEGEND FM DAURA

  3. Pingback: Sheikh Gumi ya rasa mahaifiyarsa | Neptune Prime Hausa

  4. Pingback: Sheikh Gumi ya rasa mahaifiyarsa - LEGEND FM DAURA

  5. Pingback: Gwamnan Nasarawa ya rasa ƙaninsa, watanni bayan rasuwar ɗansa | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Ƙasashen Waje

Mutumin da ya fi kowa tsallake haɗari a duniya ya mutu

Published

on

Mutumin da ya fi kowa tsallake haɗari a duniya ya mutu

Mutumin da ya fi kowa tsallake haɗari a duniya ya mutu

Daga Ibraheem El-Tafseer

Frane Selak ya kasance wanda ya fi kowa tsallake rijiya da baya a duniya.

A shekarar 1962 ya tsallake haɗarin jirgin ƙasa wanda mutane 17 suka mutu, a 1963 jirgi ya faɗi da shi kowa ya mutu sai shi kaɗai ko ƙwarzane bai yi ba.

A shekarar 1966 motar safa ta lume da su a rafi mutum huɗu sun mutu amma Frane bai samu ko ƙwarzane ba a yayin da a shekarar 1973 motarsa ta kama da wuta ya tsallake rijiya da baya, ya kuma tsallake haɗarin taho mu gama da mota ta yi da shi ya tsira ya kuma lashe yuro dubu ɗari takwas a Caca a shekarar 2003.

KU KUMA KARANTA: Labarin zuwa Hajji mai ban mamaki

Continue Reading

Rasuwa

Allah Ya yi wa matar mataimakin gwamnan Neja rasuwa

Published

on

Allah Ya yi wa matar mataimakin gwamnan Neja rasuwa

Allah Ya yi wa matar mataimakin gwamnan Neja rasuwa

Hajiya Zainab ta rasu ne a asibiti  bayan gajeruwar rashin lafiya.

Mutuwa ta riske ta ne a wani asibiti da ke Minna, babban birnin jihar a ranar Talata.

Gwamnan jihar, Mohammed Umaru Bago, ya bayyana alhini da game da wannan rashi.

Sakon ta’aziyyar da kakakinsa, Bologi Ibrahim, ya sa wa hannu ya bayyana rasuwar a matsayin babban rashi ga jihar.

KU KUMA KARANTA: Allah Ya yi wa mahaifiyar tsohon Gwamnan Borno, Ali Modu Sheriff rasuwa

Ya kuma yi addu’a Allah Ya sada ta da mafificin rahama a Aljanna Firdausi, Ya ba wa mijinta hakurin jure wannan rashi.

Continue Reading

Rasuwa

Allah Ya yi wa mahaifiyar tsohon Gwamnan Borno, Ali Modu Sheriff rasuwa

Published

on

Allah Ya yi wa mahaifiyar tsohon Gwamnan Borno, Ali Modu Sheriff rasuwa

Allah Ya yi wa mahaifiyar tsohon Gwamnan Borno, Ali Modu Sheriff rasuwa

Mahaifiyar tsohon Gwamnan Jihar Borno, Sanata Ali Modu Sheriff ta riga mu Gidan Gaskiya.

Mahaifiyar tsohon gwamnan, Hajja Aisa, ta koma ta Mahaliccinta ne a ranar Lahadi a Maiduguri, babban birnin jihar.

Ta rasu tana da shekaru 93, bayan fana da rashin lafiya.

Sanarwar rasuwar ta bayyana cewa za yi jana’izar Hajja Aisa da Azahar ranar Litinin 1 ga watan Yuli, 2024.

KU KUMA KARANTA: Allah Ya yi wa tsohuwar jarumar Kannywood, Fati Slow rasuwa

Za a yi jana’izar ne a gidant Marigayi Galadima Modu Sheriff d da ke Damboa Road a Maiduguri.
Sanarwar ta kuma roka wa marigayiyar gafara da kuma Aljannatul Firdaus.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like